Legit Hausa
Shugaban kasa Muhammadu Buhari ya ce
ya yi sallar Juma'a ne a masallacin fadar shugaban kasa a maimakon babban
masallacin kasa na Abuja saboda kaucewa cinkoson fitarsa ke janyo wa al'umma.
Mai magana da yawun shugaban kasa,
Femi Adesina ya ce shugaban kasan ya bayyana hakan ne yayin da ya ke amsa
tambaya da tawagar limamai da manyan malaman addinin musulunci daga jihohi
Najeriya suka yi masa yayin da suka kai masa ziyara a ranar Juma'a.
Tawagar limaman karkashin jagorancin
Farfesa Shehu Ahmad Galadanci sun kai ziyara gidan gwamnati ne domin su yiwa
shugaban kasar murna nasarar da ya yi a zaben shugaban kasa da aka yi a ranar
23 ga watan Fabrairu. Shugaban kasar ya ce:
"A kan batun bukatar da kuka
gabatar na nema in rinka zuwa sallar Juma'a a masallacin kasa, Ina rokon ku da
ku fahimta cewa na fara yin sallar Juma'a ne a masallacin fadar shugaban kasa
saboda in rage wahalhalun al'umma ke shiga idan na fita.
"Kamar yadda kuka sani, duk
lokacin da shugaban kasa zai fita dole sai an takaita zirga-zirga a wasu wurare
tare da kafa shinge a hanyoyi wanda hakan na iya janyo matsi ga masallata da
sauran al'umma.
" Shugaba Buhari ya gode wa
malaman bisa addu'o'i da goyon bayan da suke bawa gwamnatinsa inda ya tabbatar
musu ba zai yi kasa a gwiwa ba wurin magance kallubalen tsaro da kasar ke fama
da ita .
Ku biyo mu a Facebook facebook.com/isyakunews
Latsa nan ka shiga group din mu domin samun Labaran mu ta Whatsapp >>> https://chat.whatsapp.com/CM9VNSwQfZnIDKvffzvbiM
Domin GYARA wayarka ko FLASHING ka zo SENIORA TECH shago mai lamba 50 hawa na sama, TAUSHI PLAZA, Ahmadu Bello Way Birnin kebbi