Legit Hausa
Ministan Kasafin Kudi da Tsatsare na Kasa Sanata Udo Udoma ya ce gwamnatin tarayya tana tunanin kara harajin kayan masarufi domin ta samu ikon biyan sabon albashi mafi karanci na N30,000.
Ministan Kasafin Kudi da Tsatsare na Kasa Sanata Udo Udoma ya ce gwamnatin tarayya tana tunanin kara harajin kayan masarufi domin ta samu ikon biyan sabon albashi mafi karanci na N30,000.
Udoma ya fadi hakan ne a ranar
Talata yayin da ya bayyana a gaban kwamitin kudi majalisar dattawa.
Ministan ya kuma shaidawa kwamitin
karkashin jagorancin Sanata John Owan-Enoh cewa kwamitin kwararu masu bayar da
shawara a kan albashin mafi karanci za ta mika rahoton ta ga shugaba Muhammadu
Buhari a cikin wannan makon.
Ya ce, "Albashi mafi karanci na
N18,000 da ake biyan ma'aikata ya yi kadan sosai. Yana da matukar wahala
ma'aikata su tafiyar da rayuwar su a kan wannan kudin.
"Shugaban kasa yana goyon bayan
a sake duba batun albashin amma duk da hakan ya dace mu san cewa za mu iya
biyan albashin.
"Saboda haka ne yasa muka zo
wurin ku a majalisa domin akwai yiwuwar a yi wasu sauye-sauye musamman a
harajin kayan masarufi saboda mu samu ikon cigaba da biyan albashin da zarar an
zartas da shi.
" A yau Talata ne kuma
majalisar dattawar ta amince da N30,000 a matsayin sabon albashi mafi karanci.
An cimma wannan matsayar ne bayan kwamitin wucin gadi na sabon albashin mafi
karanci karkashin Sanata Francis Alimikhena ta mika rahoton ta.
Ku biyo mu a Facebook facebook.com/isyakunews
Latsa nan ka shiga group din mu domin samun Labaran mu ta Whatsapp >>> https://chat.whatsapp.com/CM9VNSwQfZnIDKvffzvbiM
Domin GYARA wayarka ko FLASHING ka zo SENIORA TECH shago mai lamba 50 hawa na sama, TAUSHI PLAZA, Ahmadu Bello Way Birnin kebbi
Tags:
LABARI