Legit Hausa
Hukumar shirya zabe mai zaman kanta ta kasa watau Independent National Electoral Commisslon (INEC) ta bada labarin cewa an yi zina da wasu ma'aikatan ta mata a yayin zabukan da aka gudanar satin da ya gabata na shugaban kasa da 'yan majalisar wakilai.
Hukumar shirya zabe mai zaman kanta ta kasa watau Independent National Electoral Commisslon (INEC) ta bada labarin cewa an yi zina da wasu ma'aikatan ta mata a yayin zabukan da aka gudanar satin da ya gabata na shugaban kasa da 'yan majalisar wakilai.
Wannan dai na kunshe ne a cikin wata sanarwar manema labarai
da babban jami'in yada labarai da wayar da kan masu zabe na hukumar Mista
Festus Okoye ya fitar dauke da sa hannun sa A cikin sanarwar, Mista Festus
Okoye ya bayyana cewa duk da dai zaben da aka gudanar a iya cewa an yi shi ne
cikin lumana a dukkan fadin kasar, amma dai hukumar ta dan samu tsaiko a wasu
wuraren yayin zaben.
Ya ciga da cewa hukumar ta Independent National Electoral
Commisslon (INEC) ta samu labarin tashe-tashen hankula da satar mutane da yiwa
jami'an su fyade da ma rasa rai a wasu wuraren. Haka zalika Mista Festus ya
kuma yi anfani da damar wajen jajantawa iyalan wadanda suka rasa rayukan su ko
jikkata koma rasa dukiya a wasu wuraren tare da basu hakuri da kuma tabbacin
karin matakan tsaro daga hukumar domin kaucewa kara aukuwar lamarin a gaba
DAGA ISYAKU.COM
Ku biyo mu a Facebook facebook.com/isyakunews
Latsa nan ka shiga group din mu domin samun Labaran mu ta Whatsapp >>> https://chat.whatsapp.com/CM9VNSwQfZnIDKvffzvbiM
Domin GYARA wayarka ko FLASHING ka zo SENIORA TECH shago mai lamba 50 hawa na sama, TAUSHI PLAZA, Ahmadu Bello Way Birnin kebbi