Legit Hausa
Mun samu labari cewa kam’iyyar PDP
mai adawa a jihar Kano ce ta lashe akwatin Unguwar Magwan inda nan ne
mataimakin gwamnan jihar Kano watau Dr. Nasiru Yusuf Gawuna yake zabe.
‘Dan takarar PDP, Abba Kabir Yusuf, shi ne
yayi nasara a rumfar zaben da ke Magwan da ke cikin Unguwar Gawuna a cikin
karamar hukumar Nasarawa.
Abba Yusuf ya lashe duka akwatuna 3
da ke cikin Magwan a zaben yau. Daily Trust ta rahoto PDP ta samu kuri’a 210 ne
a yankin yayin da APC mai mulki ta samu kuri’u 197. Har a akwatin da mai girma
mataimakin gwamna yake yin zabe, ‘dan takarar PDP Abba Yusuf ya doke APC da
kuri’a 3.
Jaridar tace jam’iyyar PDP ta samu
kuri’a 76 inda APC kuma ta tashi da 73 a rumfar Nasiru Gawuna da ke cikin
Magwan. A sauran akwatun yankin, PDP mai adawa ta samu 63 da 76 yayin da APC ta
iya samun kuri’u 48 da kuma 71.
A yau dinne kuma aka damke wata mota
cike makil da kayan zabe a wata makaranta da ke cikin Magwan din inda nan ne
Yankin da Mataimakin Gwamnan jihar Kano Nasiru Gawuna mai-ci ya fito.
Ku biyo mu a Facebook facebook.com/isyakunews
Latsa nan ka shiga group din mu domin samun Labaran mu ta Whatsapp >>> https://chat.whatsapp.com/CM9VNSwQfZnIDKvffzvbiM
Domin GYARA wayarka ko FLASHING ka zo SENIORA TECH shago mai lamba 50 hawa na sama, TAUSHI PLAZA, Ahmadu Bello Way Birnin kebbi