Legit Hausa
Rundunar yan sandan jihar Kano a ranar Juma’a, 22 ga watan
Fabrairu ta kama wani mamba na majalisar wakilai mai wakiltan Kiru/Bebeji,
Abdulmumin Jibrin, kan harin da aka kai wa tawagar tsohon gwamnan jihar, Rabiu
Kwankwaso.
Wasu da ake zargin yan daba ne magoya bayan dan majalisar ne
suka kai hari ga ayarin Kwankwaso. Anyi zargin cewa yan iskan sun yi wata hanya
zuwa kauyen Kofa kawanya sannan suka yi yunkurin hana masu wucewa bi ta kauyen.
Akalla mutane biyar aka kashe, yayinda wasu da dama suka ji rauni lokacin da
bangarorin biyu suka kara.
An kuma kona gidan dan majalisar, yayinda aka kona motoci
sama da 10 kurmus. An tattaro cewa mataimakin sufeto janar na yan sanda dake
Zone 1, Dan Bature da kwamishinan yan sandan jihar, Mohammed Wakili a ranar
Juma’a sun ziyarce wajen da abun ya afku sannan suka yi umurnin kama dan
majalisar.
Majiyoyin tsaro sun bayyana cewa a yanzu haka dan majalisar
na amsa tambayoyi daga hannun yan sanda a hedkwatar rundunar da ke Bompai. An
kuma tattaro cewa gwamnan jihar, Abdullahi Ganduje a ranar Laraba ya roki
kwamishinan yan sanda da kada a bari Kwankwaso ya kai gangaminsa na karshe,
amma kwamishinan yace ba zai iya hana tsohon gwamnan yancinsa ba idan har babu
kwakwaran dalili.
DAGA ISYAKU.COM
Ku biyo mu a Facebook facebook.com/isyakunews
Latsa nan ka shiga group din mu domin samun Labaran mu ta Whatsapp >>> https://chat.whatsapp.com/CM9VNSwQfZnIDKvffzvbiM
Domin GYARA wayarka ko FLASHING ka zo SENIORA TECH shago mai lamba 50 hawa na sama, TAUSHI PLAZA, Ahmadu Bello Way Birnin kebbi