Legit Hausa
Dan takarar Shugaban kasa a jam’iyyar Peoples Democratic
Party(PDP), Atiku Abubakar ya bayyana cewa yan Najeriya zai saida wa kamfanin
man fetur na Najeriya (NNPC) idan har aka zabe shi a matsayin Shugaban kasa.
Atiku ya yi watsi da rahotannin cewa yana da niyan siyar da NNPC ne ga iyalansa
sa kuma abokansa.
Dan akarar Shugaban kasa ya fayyace gaskiyar ne a lokacin
ganawa da shugabanni a jihar Kaduna. Tsohon mataimakin shugaban kasar ya kuma
bayyana cewa lallai zai siyar wa dya Najeriya da hukumar ne domin ci gaban
kasar.
“Suna ta cewa Atiku na so ya siyarwa da kanshi da abokansa
NNPC. Wannan karya ne! “Ba su so mu siyar da NNPC amma sai mun siyar da shi.
Zamu siyar maku da shi. Za ku sya? Ya tambaya." Tambayar tasa ta sa mutane
na ta ihun ‘Eh’.
A baya Legit.ng ta rahoto cewa Atiku Abubakar ya yi kira ga
'yan Najeriya su fito kwansu da kwarkwata a ranar Asabar su kayar da shugaban
kasa mai ci, Muhammadu Buhari kamar yadda suka kayar da Shugaba Goodluck
Jonathan a ranar 28 ga watan Maris na 2015. Atiku ya yi wannan furucin ne a
cikin sakon da ya fitar a faifan bidiyo a shafinsa na Twitter.
Tsohon mataimakin shugaban kasa ya ce ranar zabe rana ce da
dukkan 'yan Najeriya suke da 'yanci iri daya saboda kowa kuri'a daya ya ke da
ita. Ya bukaci 'yan Najeriya suyi zabe a kan kasancewa da cigaba da rayuwarsu
kamar yadda ta ke a cikin shekaru hudu da suka gabata ko kuma su nemi sauya
rayuwarsu da abin da yafi alheri.
DAGA ISYAKU.COM
Ku biyo mu a Facebook facebook.com/isyakunews
Latsa nan ka shiga group din mu domin samun Labaran mu ta Whatsapp >>> https://chat.whatsapp.com/KIHbQShlAs2GexpIYyxleG
Domin GYARA wayarka ko FLASHING ka zo SENIORA TECH shago mai lamba 50 hawa na sama, TAUSHI PLAZA, Ahmadu Bello Way Birnin kebbi