Yan isks sun hargitsa taron PDP a Lagos har da jifar junansu da kujeru

Legit Hausa

Wasu yan iska sunyi yunkurin hargitsa yakin neman zabe da jam'iyyar Peoples Democratic Party (PDP) ke gudanarwa a filin Tafawa Balewa (TBS) da ke jihar Lagas.

Rikici ya barke ne tsakanin wasu matasa kusa da aihanin munbarin da shuwagabanin jam’iyya ke zaune.

Lamarin, Wanda ya faru misalin karfe 1:50 na Rana, ya hada da jefe jefen kujeru da kuma fadace-fadace.

Ba a gano mussababin faruwa rikcin ba. Wadanda ke a haraban sun tsere, yayinda yan sanda suka kore yan iskan daga wajen.

Yanzu Yanzu: Rikici ya barke a gangamin PDP a Lagas inda yan daba ke ta jifan junansu da kujeru
Yanzu Yanzu: Rikici ya barke a gangamin PDP a Lagas inda yan daba ke ta jifan junansu da kujeru

Lamarin ya fara ne a lokacinda aka soma mikawa yan takaran mukaman majalisa tutar jam’iyya.

A cewar mai gabatarwa: “naga alamun wassu sun zo nan ne don tayar da hankali. Za a hukunta Wadanda suka zo nan don tada hankali a matsayin masu laifi.”

An chaje kowa kafin shiga cikin filin wasan gabannin fara shirin. Haka zalika, an hango wasu matasa na shan ganye a haraban, yayinda aka baiwa masu siyar da Kayan ruwa izinin siyar da kayan maye.

Ana kyautata zaton cewa dan takaran shugaban kasa a jam’iyyar PDP Alhaji Atiku Abubakar zai gabatar da jawabai nan da yan guntun lokaci.


Ku biyo cikin shafukan mu na zaur
Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN