Legit Hausa
A jiya, Asabar, 23 ga watan Fabarairu ne aka gudanar da
zaben shugaban kasa da 'yan majlisar tayya ('yan majalisar wakilai da dattijai)
a fadin kasar nan.
Tun a jiyan sakamako su ka fara fitowa daga mazabu
daban-daban da ke fadin kasar nan. Sai dai har yanzu hukumar zabe ta kasa
(INEC) ba ta fara fitar da sakamako a hukumance ba.
Zaben dai ya fi jan hankali ne a matakin kujerar shugaban
kasa tsakanin manyn ‘yan takara; shugaba Buhari a jam’iyyar APC da babban
abokin hamayyar sa, Atiku Abubakar, dan takarar jam’iyyar PDP. Manema labarai
da ‘yan jarida sun fi mayar da hankali a kan sakamakon mazabun manyan ‘yan
siyasa da ke goyon bayan ‘yan takarar biyu.
A yayin da aka kammala kad'a kuri'u a wasu sassa na jihohi
36 na kasar Nigeria, ciki kuwa har da jihohin Sokoto, Jigawa da Kebbi, tuni aka
fara tattara kuri'u tare da kidaya su a wasu rumfunan zabe na jihohin.
DAGA ISYAKU.COM
Ku biyo mu a Facebook facebook.com/isyakunews
Latsa nan ka shiga group din mu domin samun Labaran mu ta Whatsapp >>> https://chat.whatsapp.com/CM9VNSwQfZnIDKvffzvbiM
Domin GYARA wayarka ko FLASHING ka zo SENIORA TECH shago mai lamba 50 hawa na sama, TAUSHI PLAZA, Ahmadu Bello Way Birnin kebbi