Kotu Ta Ba INEC Umarni Ta Sa Sunayen Yan Takaran APC A Jihar Rivers


Legit Hausa

Kotun daukaka kara dake birnin Fatakwal ta bada umurnin dakatad da aiwatar da hukuncin babban kotun tarayya da ta bayar na watsi da zabubbukan fidda gwani da jam'iyyar All Progressives Congress, shiyar jihar Ribas ta gudanar.

Tun lokacin, kotun ta haramtawa hukumar gudanar da zabe ta kasa mai zaman kanta wato INEC sanya jam'iyyar APC da yan takaranta a takardan kuri'a na jihar RIbas a zaben 2019. A ranan 7 ga watan Junairu, Jastis Kolawole Omotosho ya yi watsi da dukkan zaben fidda gwani tsakanin bangaren Magnus Abe da Tonye Cole.

Yanzu haka jihar Zamfara ce ta rage ba tada yan takaran APC a zaben bana yayinda kotuna biyu daban-daban suka bayar da hukunci masu karo da juna da hallacin musharakarsu a zabe. Jigo a jam'iyyar APC, Sanata Kabiru Marafa ya ce Hukumar Zabe mai zaman kanta tayi biyaya da umurnin babban kotun Abuja inda ta yanke hukuncin cewa jam'iyyar ta APC ba za ta fitar da 'yan takara ba.

Sanatan wanda kuma shine Ciyaman din kwamitin majalisar dattawa a kan albarkatun man fetur ya yi wannan furucin ne yayin hirar da ya yi da menema labarai a babban birnin tarayya, Abuja. Ya ce INEC ta tsaya a kan bakar ta na haramtawa jam'iyyar APC reshen Zamfara fitar da 'yan takara saboda gaza gudanar da zaben fidda gwani a cikin lokacin da aka kayyade mata.


DAGA ISYAKU.COM

Ku biyo mu a Facebook facebook.com/isyakunews

Latsa nan ka shiga group din mu domin samun Labaran mu ta Whatsapp >>> https://chat.whatsapp.com/KIHbQShlAs2GexpIYyxleG

Domin GYARA wayarka ko FLASHING ka zo SENIORA TECH shago mai lamba 50 hawa na sama, TAUSHI PLAZA, Ahmadu Bello Way Birnin kebbi
Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN