Ikon Allah ne kada zai iya hana zabe a ranar Asabar 23 ga watan Fabrairu – Shugaban INEC


Legit Hausa

Shugaban hukumar zabe mai zaman kanta, Farfesa Mahmood Yakubu, yace “wani kudiri na Allah ne kadai zai iya hana gudanar da zaben Shugaban kasa da na majalisar dokoki da aka dage za a yi a ranar Asabar, 23 ga watan Fabrairu.

Shugaban na INEC ya bayyana hakan a Abuja yayinda yake jawabi ga wani taron diflomasiyya da kungiyar masu sanya idanu a zabe na kasashen duniya a Najeriya. Ikon Allah ne kada zai iya hana zabe a ranar Asabar 23 ga watan Fabrairu.

Ma’aikatar kula da harkokin waje ce ta shirya taron tare da hadin gwiwar INEC domin tattaunawa tare da abokai da kuma takwarorin Najeriya kan zaben da aka dage. 

Yakubu wanda ya samu wakilcin wani kwamishinar INEC, Dr Mustapha Lecky ya bayyana cewa hukumar ta tanadi komai domin tabbatar da gudanr da zaben a ranar Asabar. Shugaban INEC ya bayyana cewa hukumar bata da wani dalili da take ganin cewa wani abu zai daktar da zaben ranar 23 ga watan Fabrairu.
 

DAGA ISYAKU.COM

Ku biyo mu a Facebook facebook.com/isyakunews

Latsa nan ka shiga group din mu domin samun Labaran mu ta Whatsapp >>> https://chat.whatsapp.com/KIHbQShlAs2GexpIYyxleG

Domin GYARA wayarka ko FLASHING ka zo SENIORA TECH shago mai lamba 50 hawa na sama, TAUSHI PLAZA, Ahmadu Bello Way Birnin kebbi
Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN