Type Here to Get Search Results !

Ikon Allah ne kada zai iya hana zabe a ranar Asabar 23 ga watan Fabrairu – Shugaban INEC


Legit Hausa

Shugaban hukumar zabe mai zaman kanta, Farfesa Mahmood Yakubu, yace “wani kudiri na Allah ne kadai zai iya hana gudanar da zaben Shugaban kasa da na majalisar dokoki da aka dage za a yi a ranar Asabar, 23 ga watan Fabrairu.

Shugaban na INEC ya bayyana hakan a Abuja yayinda yake jawabi ga wani taron diflomasiyya da kungiyar masu sanya idanu a zabe na kasashen duniya a Najeriya. Ikon Allah ne kada zai iya hana zabe a ranar Asabar 23 ga watan Fabrairu.

Ma’aikatar kula da harkokin waje ce ta shirya taron tare da hadin gwiwar INEC domin tattaunawa tare da abokai da kuma takwarorin Najeriya kan zaben da aka dage. 

Yakubu wanda ya samu wakilcin wani kwamishinar INEC, Dr Mustapha Lecky ya bayyana cewa hukumar ta tanadi komai domin tabbatar da gudanr da zaben a ranar Asabar. Shugaban INEC ya bayyana cewa hukumar bata da wani dalili da take ganin cewa wani abu zai daktar da zaben ranar 23 ga watan Fabrairu.
 

DAGA ISYAKU.COM

Ku biyo mu a Facebook facebook.com/isyakunews

Latsa nan ka shiga group din mu domin samun Labaran mu ta Whatsapp >>> https://chat.whatsapp.com/KIHbQShlAs2GexpIYyxleG

Domin GYARA wayarka ko FLASHING ka zo SENIORA TECH shago mai lamba 50 hawa na sama, TAUSHI PLAZA, Ahmadu Bello Way Birnin kebbi

Top Post Ad

Below Post Ad

Shiga group dinmu na WhatsApp domin samun labaran mu kai tsaye LATSA NAN
Domin zama Wakilin mu a garin ku LATSA NAN
Domin aiko Sako/Labari/Korafi LATSA NAN
Domin samun labaran mu a Facebook LATSA NAN
Domin samun labaranmu a Twitter LATSA NAN