Legit Hausa
Dan takarar neman zama shugaban kasar Najeriya a karkashin
inuwar jam’iyyyar adawa ta PDP, Atiku Abubakar, ya yi zargin cewar ana shirin
sake daga zabe a jihohin Adamawa, Borno da Kaduna.
A jawabin da mai taimaka ma sa a bangaren yada labarai,
Phrank Shuaibu, ya fitar a jiya, Talata, Atiku ya yi zargin cewar za a daga
zabe a jihohin ne domin ganin cewar an shirya magudin da zai bawa shugaba
Buhari nasara a zaben da za a gudanar, Ya yi gargadin cewar duk wani yunkuri na
daga zabe a wata jiha daidai yak e da magudin zabe, bangar siyasa da yunkurin
tayar da rikici da jam’iyyar PDP ba za ta lamunta ba.
“Daga cikin abubuwan da su ka kulla a ganawar shugaban kasa
da gwamnoni da kuma shugabannin tsaro akwai batun ganin yadda za a daga zabe a
jihohin Adamawa, Borno da Kaduna ta hanyar fake wa da dalilan tsaro domin bawa
jam’iyyar APC damar aikata magudin idan an zo sake gudanar da zabe a jihohin.
“Kalaman shugaban Buhari ga ‘yan Najeriya a kan gudanar da
sahihin zabe na adalci za su zama yaudara idan haka ta tabbata,” a cewar Atiku.
Ya kara da cewa, “wannan makircin da su ke shirya w aba zai
hana jam’iyyar PDP bacci ba, saboda ikon tsamo Najeriya daga mulkin kama karya
ya na hannun ‘yan kasa ne ba wasu tsirarun gwamnonin APC da ke son Buhari ya
zarce a mulki ta kowanne hali ba.”
Atiku ya cigaba da cewa, “gudanar da sahihin zabe na gaskiya
a 2019 shine abu ma fi cancanta ga jaririyar siyasar Najeriya.” Wannan ba shine
karo na farko da jam’iyyar PDP da dan takarar ta ke zargin cewar ana shirya ma
su magudi a zaben shekarar 2019 ba. Sai dai jam’iyyar APC mai mulki ta ce PDP
da dan takarar ta na yin wadannan korafe-korafe ne saboda sun san ba za su yi
nasara a zabukan da za a gudanar ba.
DAGA ISYAKU.COM
Ku biyo mu a Facebook facebook.com/isyakunews
Latsa nan ka shiga group din mu domin samun Labaran mu ta Whatsapp >>> https://chat.whatsapp.com/KIHbQShlAs2GexpIYyxleG
Domin GYARA wayarka ko FLASHING ka zo SENIORA TECH shago mai lamba 50 hawa na sama, TAUSHI PLAZA, Ahmadu Bello Way Birnin kebbi