Idan APC Bata Yi Takara Ba A Zamfara, Wa Zai Fi Amfana ?


Hausa.leadership.ng

Yanzu haka dai hukumar zabe mai zaman kanta, INEC, ta tabbatar da cewa jam’iyyar APC ba ta da ’yan takara yayin zaben mai zuwa a jihar Zamfara bayan da ta bayar da sanarwar jerin sunayen halastattun ’yan takarar da ta ce za su shiga zaben na 2019, wanda za a gudanar a ranar 16 ga watan nan da kuma 2 ga watan gobe, wato Maris.

Hakan ya biyo bayan yadda INEC din ta ce APC mai mulkin jihar ba ta gudanar da halastaccen zaben cike gurbi ba har zuwa lokacin da wa’adin yin hakan ya kare, kamar yadda hukumar ta bayar da umarni. Kodayake dai wasu bangarori sun daukaka kan wannan mataki da hukumar zaben ta dauka, amma abin damuwar shi ne, zai yi wahala a kammala karkare wannan takaddama da a shafe ’yan watanni a na yin ta kafin gudanar da manyan zabukan kasar, wanda hakan ke nuna cewa, za a iya gudanar da zaben ba tare da ’yan takarar APC ko guda daya ba.

To, babban abin tashin hankali ga jam’iyyar shi ne, idan har a ka kuskura a ka gudanar da zabe ba tare da ’yan takarar jam’iyyar sun shiga ba, to zai yi wahala su iya samun hurumin shigar da kara a gaban kotu kan zaben da ba a yi shi da su ba. Sai dai kuma idan hakan ta iya wakana har su ka yi galaba a kotu nan gaba, musamman bayan rantsar da sabuwar gwamnati, to hakan ya na nufin za a sake rushe dukkanin zababbun jihar kenan, ciki kuwa har da kakakin majalisar dokokin jihar, wanda kundin tsarin mulki ya ce shi ke da alhakin rikon jihar a duk lokacin da a rasa kowa a kujerar gwamna da ta mataimakinsa.

A nan sai dai babban jojin jihar ya amshi riko kenan na tsawon kwanaki 90 da doka ta tanada, kafin a gudanar da sabon zabe. Kada a manta da cewa a lokacin da hakan za ta faru, ba APC ke mulkin jihar ba kuma babu wani nata da ke rike da mukami, illa dai majalisar zartarwa jam’iyyar da ta kafa gwamnati a wannan zabe da ke tafe, wanda hakan zai iya yin tasiri gare ta, idan a ka yi amfani da kwamishinonin da a ka nada.

Tambayarmu a nan ita ce, shin wa zai fi amfana, idan APC ba ta yi takara a Zamfara ba? akwai manyan ’yan takara guda biyu da a ke ganin sun fi sauran karfi bisa wasu dalilai da wakilinmu a Zamfara ya nazarto ma na. Yanzu haka tauraruwar ‘yan takara jam’iyyar PDP da NRM da PDP ke haskawa a jihar Zamfara kuma su ke ta damawarsu babu dare babu rana.

A yanzu haka masu fashin bakin siyasar jihar Zamfara na ganin cewa wadannan ‘yan takarar ne za su fafata a tsakaninsu matukar APC ba ta shigo ba. Sanata Saidu Muhammad Dansadau shi ne dan takarar gwamna a jam’iyyar NRM na jihar Zamfara, yanzu haka ya na daya daga cikin wadanda tauraruwar sa ke haskawa a jihar da ‘yan takarar majalisar dattawa da ‘yan majalisar dokoki na kasa da na jiha. 

Don yanzu haka babu lungo da sako da ba su kutsa ba kuma abinda masu ruwa da tsaki a harkar siyasa ke cewa, Sanata Dansadau tauraruwarsa na haskawa ne sakamakon yadda ya ke kalubalantar gwamnatin jihar Zamfara da ta tarayya a kan yadda a ke kashe mutane babu dare babu rana a jihar, inda shi ne kadai ke ta fita cikin kafafen yada labarai ya na kalubalantar gwamnati har ya na cewa, “ita gwamnatin ta san masu kashe mutane, ta gaza daukar mataki.” Sanata Kabir Marafa ya bayyana cewa idan APC ba ta samu ‘yan takara ba, to a matsayinsa na Kabiru zai mara wa daya daga cikin ‘yan takarar da yanzu haka a ke da su a cikin jihar mai irin akida tasa.

Wasu masana na hasashen cewa Sanata Kabir Marafa zai iya marawa Sanata Dansadau baya domin akidarsu daya ta adawa da gwamnatin jihar Zamfara da shi kansa Gwamna Abdulaziz Yari a kan tabarbarewar tsaron jihar da kuma halin ko’ inkula da a ke ganin ya ke nunawa, idan annoba ta samu al’ummar jihar. Da alama wannan goyon baya da a ke tsammanin Marafa zai bai wa Dansadau, zai ba shi tagomashi mai yawa da karkatar da tunanin al’ummar jihar ga goyan bayansa a zaben gwamna shi da jama’ar shi, don a na ganin da ma burin Sanata Marafa shi ne ya yi wa Gwamna Yari da mukarrabansa ritayar dole da shi kansa sanata.

A yanzu haka ga alamu wannan hasashen masana na neman tabbata, don yanzu haka an fara hada fastar Sanata Dansadau a matsayin dan takarar gwamna da Muhammad Buhari a matakin shugaban kasa. Lallai wannan wake da shinkafa tsakanin Tsintsiya da Zuma zai kawo sauyi da fasali a siyasar jihar Zamfara. A bangare daya kuma, Hon. Bello Muhammad Matawalle, dan takarar gwamna a jam’iyyar PDP na jihar Zamfara, shi ma yanzu ya na daya daga cikin wadanda tauraruwarsu ke haskawa ga Zamfarawa, musamman ma wannan ba shi ne karonsa na farko ba wajen tsaya wa takara a zaben gwamnan jihar Zamfara ba.

Kuma yanzu haka ya shiga yakin sunkuru, babu dare babu rana, wajen neman ganin ya samu nasara a zabe mai zuwa. Masu Ruwa da tsaki a harkar siyasa jihar Zamfara su na ganin idan Sanata Kabir Marafa ya marawa Sanata Saidu Muhammad Dansadau baya sakamakon rashin dan takarar a APC, shi kuma Gwamna Yari ya mara wa dan takarar na PDP baya, to Matawalle zai iya kai labari, domin da ma a siyasarsu gida daya su ka fito, wato gidan Sanata Ahmad Sani Yariman Bakura kuma Allah ya albarkaci Hon Matawalle da kyauta ga al’umma, kamar Yariman, domin a na ganin shi kullum hannunsa a sake ya ke wanda ba ya ‘kabalu’, kuma irin shi wasu ne jama’a ke bukata.

Hakan kuma karfin da PDP ke da shi a karan-kanta a jihar na kasancewarta babbar jam’iyyar adawa a jihar tsawon shekara da shekaru zai taimaka wa tafiyar dan takarar nata, idan APC ba ta yin takara, Wasu masanan na ganin cewa, kwarjinin Matawalle ga Zamfarawa zai sa ya samu nasarar zabe koda babu wanda da goya da shi, domin wasu na ganin cewa ba zai aminta da gwamnatin ta shigo cikinsu ba, don za ta bata ma sa tsari. Idan kuma ta yi ma sa kutse zai samu matsala ba, tunda dai dan takarar gwamnati ne ba a so kuma shi an san ba na gwamnati ba ne, domin a zaben da ya gabata da shi ne Gwamna Yari ya fafata, wanda ba don guguwar Buhariyya da APC ba, a na ganin Yari ba zai kai labari a 2015 ba. Yanzu dai kallo ya koma sama tunda shaho ya dau giwa!

DAGA ISYAKU.COM 

Ku biyo mu a Facebook facebook.com/isyakunews 

Latsa nan ka shiga group din mu domin samun Labaran mu ta Whatsapp >>> https://chat.whatsapp.com/KIHbQShlAs2GexpIYyxleG 

Domin GYARA wayarka ko FLASHING ka zo SENIORA TECH shago mai lamba 50 hawa na sama, TAUSHI PLAZA, Ahmadu Bello Way Birnin kebbi
Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN