Dattawan Arewa, Afenifere Da Ohanaeze Sun Ayyana Goyon Bayansu Ga Atiku


Hausa.leadership.ng

Kungiyoyin tuntuba na al’ummun Nijeriya da suka hada da kungiyar dattawan Yarbawa ta Afenifere, da Ohanaeze Ndigbo ta kabilar Igbo, da kuma kungiyar dattawan arewa wato (Northern Elders Forum) sai kungiyar arewa masu tsakiya da ta hadin kan ‘yan Neja-delta, sun ayyana dan takarar shugaban kasa karkashin inuwar jam’iyyar PDP, wato Alhaji Atiku Abubakar a matsayin dan takarar da zasu goya ma baya.

Kungiyoyin suna cikin tsakiyar gabatar da taron nasu ne a babban otel din Sheraton da ke Abuja, inda suka ayyana Alhaji Atiku Abubakar a matsayin wanda yafi cancanta da shugabancin kasar nan, don haka dole su fito karara don ayyana shi a matsayin wanda zasu goya ma baya a zabukkan shekarar 2019.

 Jagororin kungiyoyin sun hada da Cif Ayo Adebanjo, Cif Nnia Nwodo, Farfesa Ango Abdullahi, Cif Edwin Clark da kuma Dakta Bitrus Pogu, sun bukaci ‘yan Nijeriya da su zabi jami’iyyar PDP a zaben da za a gudanar a ranar 16 ga watan Fabrairu da muke fuskanta.

DAGA ISYAKU.COM 

Ku biyo mu a Facebook facebook.com/isyakunews 

Latsa nan ka shiga group din mu domin samun Labaran mu ta Whatsapp >>> https://chat.whatsapp.com/KIHbQShlAs2GexpIYyxleG 

Domin GYARA wayarka ko FLASHING ka zo SENIORA TECH shago mai lamba 50 hawa na sama, TAUSHI PLAZA, Ahmadu Bello Way Birnin kebbi
Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN