Babu yadda za a gudanar da zabe a jihar Zamfara ba tare da 'yan takaran APC ba - Gwamna Yari

Gwamna Abdulazeez Yari ya yi barazanar cewa babu yadda za a gudanar da zabe a jihar Zamfara matukar hukumar zabe INEC bata saka sunayen yan takaran jam'iyar APC ba a jerin sunayen 'yan takara da za su yi zabe a jihar.

Yari ya yi wannan zancen ne a garin Talata Mafara ranar Juma'a yayin yakin neman zabe a karamar hukumar a gaban dimbin magoya bayan jam'iyar APC.

Gwamnan ya ce " Babu yadda za a gudanar da zabuka a jihar Zamfara ba tare da yan takaran jam'iyar APC ba duk da cewa aabban Kotun jihar Zamfara ta tabbatar da APC ta gudanar da zaben fitar da gwani".
 
" Mun dogara ne da hukuncin da babban Kotun Zamfara ta yanke kan shari'ar cewa APC ta gudanar da zaben fitar da gwani a Zamfara kuma ta bayar da umarni cewa INEC ta saka sunayen 'yan takarar APC a zabukan da za a yi".

Idan dai baku manta ba, INEC ta ce APC bata gudanar da zaben fitar da gwani ba a Zamfara, sakamakon haka bata gabatar da sunayen 'yan takaranta ba ga INEC kafin wa'adin ranar 7 ga watan Oktoba 2019.

DAGA ISYAKU.COM

Ku biyo mu a Facebook facebook.com/isyakunews

Latsa nan ka shiga group din mu domin samun Labaran mu ta Whatsapp >>> https://chat.whatsapp.com/KIHbQShlAs2GexpIYyxleG

Domin GYARA wayarka ko FLASHING ka zo SENIORA TECH shago mai lamba 50 hawa na sama, TAUSHI PLAZA, Ahmadu Bello Way Birnin kebbi
Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN