Type Here to Get Search Results !

Babu yadda za a gudanar da zabe a jihar Zamfara ba tare da 'yan takaran APC ba - Gwamna Yari

Gwamna Abdulazeez Yari ya yi barazanar cewa babu yadda za a gudanar da zabe a jihar Zamfara matukar hukumar zabe INEC bata saka sunayen yan takaran jam'iyar APC ba a jerin sunayen 'yan takara da za su yi zabe a jihar.

Yari ya yi wannan zancen ne a garin Talata Mafara ranar Juma'a yayin yakin neman zabe a karamar hukumar a gaban dimbin magoya bayan jam'iyar APC.

Gwamnan ya ce " Babu yadda za a gudanar da zabuka a jihar Zamfara ba tare da yan takaran jam'iyar APC ba duk da cewa aabban Kotun jihar Zamfara ta tabbatar da APC ta gudanar da zaben fitar da gwani".
 
" Mun dogara ne da hukuncin da babban Kotun Zamfara ta yanke kan shari'ar cewa APC ta gudanar da zaben fitar da gwani a Zamfara kuma ta bayar da umarni cewa INEC ta saka sunayen 'yan takarar APC a zabukan da za a yi".

Idan dai baku manta ba, INEC ta ce APC bata gudanar da zaben fitar da gwani ba a Zamfara, sakamakon haka bata gabatar da sunayen 'yan takaranta ba ga INEC kafin wa'adin ranar 7 ga watan Oktoba 2019.

DAGA ISYAKU.COM

Ku biyo mu a Facebook facebook.com/isyakunews

Latsa nan ka shiga group din mu domin samun Labaran mu ta Whatsapp >>> https://chat.whatsapp.com/KIHbQShlAs2GexpIYyxleG

Domin GYARA wayarka ko FLASHING ka zo SENIORA TECH shago mai lamba 50 hawa na sama, TAUSHI PLAZA, Ahmadu Bello Way Birnin kebbi

Top Post Ad

Below Post Ad

Shiga group dinmu na WhatsApp domin samun labaran mu kai tsaye LATSA NAN
Domin zama Wakilin mu a garin ku LATSA NAN
Domin aiko Sako/Labari/Korafi LATSA NAN
Domin samun labaran mu a Facebook LATSA NAN
Domin samun labaranmu a Twitter LATSA NAN