Type Here to Get Search Results !

Main event

An kashe jami'an hukumar NDLEA guda hudu a wata jihar kudu

Wasu da ba'a san ko su waye ba sun kashe jami'an hukumar hana sha da tu'ammali da miyagun kwayoyi NDLEA guda hudu yayin da suke gudanar da aikinsu a jihar Ondo ranar Lahadi.

Majiyar ISYAKU.COM ta ce wasu mutane ne a kan babura suka nufi wajen da jami'an suke gudanar da aikin tsayar da ababen hawa suna bincike, sai suka bude masu wuta da bindigogi, kuma suka kone motar jami'an kirar Hilux.

Daya daga cikin hafsoshin guda biyar ya tsira da ransa, amma hudu daga cikinsu sun mutu nan take. Tuni sauran jami'an tsaro suka isa wajen da lamarin ya faru domin bincike da farautar wadanda suka aiikata wannan danyen aiki duba da cewa maharan sun yi awon gaba da bindigogin jami'an na NDLEA.

DAGA ISYAKU.COM 

Ku biyo mu a Facebook facebook.com/isyakunews 

Latsa nan ka shiga group din mu domin samun Labaran mu ta Whatsapp >>> https://chat.whatsapp.com/KIHbQShlAs2GexpIYyxleG 

Domin GYARA wayarka ko FLASHING ka zo SENIORA TECH shago mai lamba 50 hawa na sama, TAUSHI PLAZA, Ahmadu Bello Way Birnin kebbi

Top Post Ad

Below Post Ad

Shiga group dinmu na WhatsApp domin samun labaran mu kai tsaye LATSA NAN
Domin zama Wakilin mu a garin ku LATSA NAN
Domin aiko Sako/Labari/Korafi LATSA NAN
Domin samun labaran mu a Facebook LATSA NAN
Domin samun labaranmu a Twitter LATSA NAN

Hollywood Movies