An buga gangar yaki tsakanin kasashen Idiya da Pakistan

A jiya Laraba ne dai kasashen Pakistan da Indiya suka mayarwa da juna martani ta hanyar jijjigo jiragen juna bayan harin makonnin baya-bayan nan da ya hallaka sojin Indiya da dama Kasashen Pakistan da Indiya sun yi ikirarin kakkabo jiragen yakin juna, a wani rikici da ke da da kamari tsakaninsu, kuma ake fargabar cewa za a samu fito na fito tsakanin kasashen makwabtan juna masu makaman nukiliya. Kasashen biyu dai na kai ruwa rana ne kan yankin Kashmir da ke karkashin ikon Indiya, lamarin da ya yi sanadiyar hassala rikicin da ke tsakaninsu a karon farko cikin shekaru 20. Kakakin ma’aikatar tsaron Indiya, Raveesh Kumar, a yau Laraba ya ce an fara zube-ban kwarya ne, bayan da sojin Pakistan suka fara kai hari kan sojin da Indiya ta girke a yankin Kashmir. A bangare guda Firaministan Pakistan, Imran Khan wanda ya nemi kasashen biyu su tattauna don samar da mafita, ya ce duk da haka Pakistan ba za ta tsaya ta na kallo ba, don kuwa za ta dauki matakan da suka dace don kare kanta. Firaminista Imran Khan ya kuma bayyana yadda jiragen yakin Indiya suka ratsa kasarsa ba tare da izini ba, matakin da ya tilasta su kakkabo jiragen tare da kame matukansu. Rikicin ya tashi ne bayan wani harin bam da ya yi sanadin mutuwar dakarun Indiya 40 a yankin Kashmir ranar 14 ga watan Fabarairu, hari mafi muni cikin shekaru 30 na rikicin tsakanin India da Pakistan.

Read More at: https://hausa.leadership.ng/2019/02/28/an-buga-gangar-yaki-tsakanin-kasashen-pakistan-da-indiya/
 Leadership Hausa


A jiya Laraba ne dai kasashen Pakistan da Indiya suka mayarwa da juna martani ta hanyar jijjigo jiragen juna bayan harin makonnin baya-bayan nan da ya hallaka sojin Indiya da dama Kasashen Pakistan da Indiya sun yi ikirarin kakkabo jiragen yakin juna, a wani rikici da ke da da kamari tsakaninsu, kuma ake fargabar cewa za a samu fito na fito tsakanin kasashen makwabtan juna masu makaman nukiliya.


Kasashen biyu dai na kai ruwa rana ne kan yankin Kashmir da ke karkashin ikon Indiya, lamarin da ya yi sanadiyar hassala rikicin da ke tsakaninsu a karon farko cikin shekaru 20. Kakakin ma’aikatar tsaron Indiya, Raveesh Kumar, a yau Laraba ya ce an fara zube-ban kwarya ne, bayan da sojin Pakistan suka fara kai hari kan sojin da Indiya ta girke a yankin Kashmir.


A bangare guda Firaministan Pakistan, Imran Khan wanda ya nemi kasashen biyu su tattauna don samar da mafita, ya ce duk da haka Pakistan ba za ta tsaya ta na kallo ba, don kuwa za ta dauki matakan da suka dace don kare kanta.


Firaminista Imran Khan ya kuma bayyana yadda jiragen yakin Indiya suka ratsa kasarsa ba tare da izini ba, matakin da ya tilasta su kakkabo jiragen tare da kame matukansu. Rikicin ya tashi ne bayan wani harin bam da ya yi sanadin mutuwar dakarun Indiya 40 a yankin Kashmir ranar 14 ga watan Fabarairu, hari mafi muni cikin shekaru 30 na rikicin tsakanin India da Pakistan.


DAGA ISYAKU.COM

Ku biyo mu a Facebook facebook.com/isyakunews

Latsa nan ka shiga group din mu domin samun Labaran mu ta Whatsapp >>> https://chat.whatsapp.com/CM9VNSwQfZnIDKvffzvbiM

Domin GYARA wayarka ko FLASHING ka zo SENIORA TECH shago mai lamba 50 hawa na sama, TAUSHI PLAZA, Ahmadu Bello Way Birnin kebbi
Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN