Legit Hausa
Gwamnan jihar Ogun, Ibikunle Amosun ya bugi kirji ya ce dan
takarar gwamna na jam'iyyar Allied Peoples Movement (APM), Adekunle Akinlade ne
zai lashe zabe a jihar. Mr Amosun ya kuma shawarci gwamnatin tarayya kada ta
aike da sojoji zuwa jihar domin zabe duk da ya bayar da tabbacin za a gudanar
da zaben lami lafiya.
Gwamnan ya yi wannan jawabin ne a daren ranar Litinin a
taron murnar shiga sabuwar shekara da akayi a Oke-Ilewo a garin Abeokuta.
Gwamna Amosun yana takarar kujerar sanata a karkashin jam'iyyar All
Progressives Congress amma yana goyon bayan Mr Akinlade wadda ya sauya sheka
zuwa jam'iyyar APM bayan ya sha kaye a hannun Dapo Abiodun.
Mr Amosun ya ce na hannun damarsa, Mr Akinlade zai kayar da
Mr Abiodun da sauran 'yan takarar gwamna a zaben da za a gudanar a watan Mayu.
Gwamnan mai barin gadon ya yi kira ga al'ummar jihar su rungumi zaman lafiya
musamman a wannan lokacin da zabe ke qaratowa.
"Mu hada hannu wuri guda domin nunawa duniya cewa mu
mutane ne masu son zaman lafiya kuma jiha ce wadda ta samar da fittatun mutane
a Najeriya," a cewar Mr Amosun. "Mu nuna musu cewa bamu bukatar
sojoji ko 'yan sanda saboda zabe domin zamu gudanar da zaben mu cikin zaman
lafiya da lumana. Sannan ku matasa, duk wanda ya nemi kuyi masa bangar siyasa
ke fada masa ya turo yaransu kuyi bangar tare."
A yanzu da ya ke shirin barin mukaminsa na gwamna, Mr Amosun
ya mika godiyarsa ga dukkan al'ummar jihar saboda irin gudunmawar da suka bashi
har ta kai ga ya samu nasarorin da ya samu a jihar.
DAGA ISYAKU.COM
Ku biyo mu a Facebook facebook.com/isyakunews
Latsa nan ka shiga group din mu domin samun Labaran mu ta Whatsapp >>> https://chat.whatsapp.com/KIHbQShlAs2GexpIYyxleG
Domin GYARA wayarka ko FLASHING ka zo SENIORA TECH shago mai lamba 50 hawa na sama, TAUSHI PLAZA, Ahmadu Bello Way Birnin kebbi