Yan boko haram sun kone gonakin shinkafa na bayin Allah a Borno

RFI Hausa

Mayakan Boko Haram sun kone wasu gonakin shinkafa a kauyen Zabarmari da ke karamar hukumar Jere ta jihar Borno, lamarin da ya haddasa tafka hasarar daruruwan buhunan shinkafa da aka noma a daminar bana.

Malam Hassan Zabarmari shi ne shugaban manoman da matsalar ta shafa, wanda ya shaidawa sashin Hausa na RFI cewa yawan hasarar da suka yi ta wuce matakin kayyadewa sai dai kawai su kiyasta.


A cewar Hassan Zabarmari mayakan na Boko Haram sun kone sama da kadada ko fadin kasar da ya zarce eka 250 na gonaki.


Shugaban manoman ya ce akwai bukatar gwamnati ta gaggauta kawo musu dauki la’akari da halin kuncin da harin kone musu gonakin ya jefa su.

DAGA ISYAKU.COM

Ku biyo mu a Facebook facebook.com/isyakunews

Latsa nan ka shiga group din mu domin samun Labaran mu ta Whatsapp >>> https://chat.whatsapp.com/KIHbQShlAs2GexpIYyxleG

Domin GYARA wayarka ko FLASHING ka zo SENIORA TECH shago mai lamba 50 hawa na sama, TAUSHI PLAZA, Ahmadu Bello Way Birnin kebbi
Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN