Mai Martaba Sarkin Kano zai ba Naziru Ahmad Sarkin Mawaka

 RFI Hausa

Fadar mai martaba sarkin Kano dake Najeriya, ta sanar da nada shahararen mawaki Nazir Ahmad a matsayin Sarkin Mawakan Sarkin Kano Muhammadu Sunusi Na biyu.

Cikin wata sanarwa mai dauke da sa hannun shugaban ma'aikatan Fadar Kanon Munir Sunusi, tace lura da gudummowar daya baiwa Sarkin Kano tun yana matsayin Dan Majen Kano, da kuma zamowarsa Sarki, yasa ya fadar girmama shi da wannan sarauta ta Sarkin mawaka.

Shi dai mawaki Nazir Ahmad ya shahara ta fuskar wakokin Sarakuna da fitattun attajirai a arewacin Najeriya amma da salon zamani, zalika yayi wasu wakokin da suka fita a fina-finan hausa

An tsaida 27 ga Watan Disamba a matsayin ranar da za'ayi bikin nadin sarautar a fadar Masarautar Kano.

DAGA ISYAKU.COM

Ku biyo mu a Facebook facebook.com/isyakunews

Latsa nan ka shiga group din mu domin samun Labaran mu ta Whatsapp >>> https://chat.whatsapp.com/KIHbQShlAs2GexpIYyxleG

Domin Gyara Wayarka Ka ko FLASHING ka zo SENIORA TECH shago mai lamba 50 hawa na sama, TAUSHI PLAZA, Ahmadu Bello Way Birnin kebbi

Post a Comment

RUBUTA SHARHI KO RA'AYINKA KAN WANNAN LABARI

Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN