Madalla, yansanda sun kubutar da wata mata da aka yi garkuwa da ita, duba abin da ya faru

Wadansu masu satar mutane domi su yi garkuwa da su a babban titin Ogbakiri zuwa Buguma a jihar Rivers sun gamu da mumunar ajali a hannun jami'an yansanda bayan yansanda sun gano maboyarsu, suka kai masu farmaki kuma suka halaka su nan take kuma aka kubutar da wata ma'aikaciyar jinya Nurse yan bindigar da suka yi garkuwa da ita.

Yan bindigar sun sace ma'aikaciyar Asibitin ne tun ranar Laraba da ta gabata, amma sai ranar Talata aka kubutar da ita bayan jami'an yansanda na F-SARS sun yi ma yan bindigar diran mikiya kuma suka halaka su.

Wannan ya biyo bayan wani rahotun sirri ne da jami'an sashen ayyukan asirin kan yan fashi da makami da kuma sace mutane domin a yi garkuwa da su suka samar cikin lokaci, kan inda yan fashin suke bayan an yi amfani da kimiyyar zamani na sadarwa domin a gano hakikanin inda yan bindigar suka boye.

DAGA ISYAKU.COM

Ku biyo mu a Facebook facebook.com/isyakunews

Latsa nan ka shiga group din mu domin samun Labaran mu ta Whatsapp >>> https://chat.whatsapp.com/KIHbQShlAs2GexpIYyxleG

Domin GYARA wayarka ko FLASHING ka zo SENIORA TECH shago mai lamba 50 hawa na sama, TAUSHI PLAZA, Ahmadu Bello Way Birnin kebbi
Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN