Duba abin da dabbobi ke yi wa postocin shugaba Buhari a wata jihar PDP

Jam'iyar APC a jihar Abia ta koka kan yadda ta yi zargin jam'iyar adawa mai mulki a jihar tana amfani da yan daban siyasa da dabbobi, domin wulakanta postocin kampen na shugaba Muhammadu Buhari da dan takarar kujerar Gwamna a jihar karkashin jam'iyar APC  Dr. Uche Ogah a babban birnin jihar Umuahia.

The Nation ta ruwaito cewa wani jigo a jam'iyar APC a jihar Comrade Benedict Godson ya ce, jam'iyar APC ba za ta lamunta da irin wannan hali na takala ba bayan ya zargi jam'iyar PDP a jihar da daukar dawainiyar takala da ake yi ma yan APC.

A wani hoto da ya bayyana ma an ga awaki suna cin takardun postocin shugaba Buhari a birnin Umuahia na jihar Abia.

DAGA ISYAKU.COM

Ku biyo mu a Facebook facebook.com/isyakunews

Latsa nan ka shiga group din mu domin samun Labaran mu ta Whatsapp >>> https://chat.whatsapp.com/KIHbQShlAs2GexpIYyxleG

Domin GYARA wayarka ko FLASHING ka zo SENIORA TECH shago mai lamba 50 hawa na sama, TAUSHI PLAZA, Ahmadu Bello Way Birnin kebbi
Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN