Legit Hausa
Hukumar 'yan sandan Najeriya reshen jihar Zamfara ta bayar a
sanarwar takaita zirga-zirga a karamara hukumar Tsafe da ke jihar sakamakon
zanga-zangar nuna damuwa kan yawaitar kashe-kashe a jihar wadda daga bisani ya
haifar da rudani da kone-kone.
Jaridar Punch ta ruwaito cewa wasu matasa sun fito suna
zanga-zangar nuna damuwar su kan lamarin rashin tsaro a jihar inda aka ce sun
rufe tittin da ya sada Funtua, Zaria, Sokoto, Kebbi da Kaduna. Rahotanni sun ce
matasan sun kona sakatariyar karamar hukumar Tsafe kuma sun nufi gidan shugaban
karamar hukumar.
Matasan sun rera wakar, "jiki magayi, sai mun canja
Buhari", kamar yadda zaku iya gani a cikin Jami'n hulda da jama'a na 'yan
sandan jihar, Mohammad Shehu ya sanar da cewar an al'umma za su iya fitowa suyi
harkokinsu ne daga karfe 7 na safe zuwa karfe 6 na yamma kamar yadda TheCable
ta ruwaito.
Ya ce dokar takaita zirga-zirgar za ta cigaba da aiki har
sai nan gaba idan abubuwan sun lafa a garin. 'Yan ta'adda sun kai hari a kauyen
Magami da ke karamar hukumar Maradun a ranar Asabar inda suka kashe mutane da
dama.
DAGA ISYAKU.COM
Ku biyo mu a Facebook facebook.com/isyakunews
Latsa nan ka shiga group din mu domin samun Labaran mu ta Whatsapp >>> https://chat.whatsapp.com/KIHbQShlAs2GexpIYyxleG
Domin GYARA wayarka ko FLASHING ka zo SENIORA TECH shago mai lamba 50 hawa na sama, TAUSHI PLAZA, Ahmadu Bello Way Birnin kebbi