Sakon Buhari ga shugabannin kasashen gefen tekun Chadi

Legit Hausa

Shugaba Muhammadu Buhari ya kalubanci ragowar shugabannin kasashen gefen tekun Chadi (LBC) a kan kara rubanya kokarinsu a bangaren yaki da 'yan ta'addar kungiyar Boko Haram. Buhari ya yi wannan kira ne a yau, Alhamis, yayin halartar taron shugabannin kasashen gefen tekun Chadi a birnin N'Dajamena.

"Ba zamu saurara ko mu bar makiya yankin mu su sukurkuta zaman lafiya a kasashen mu ba. Dole mu kara kokarinmu domin korar ta'addanci daga yankinmu." "Dole mu tashi tsaye wajen samar da zaman lafiya da cigaba mai dorewa.

A wannan gaba ne nake bukatar mu hada karfi da karfe domin ganin mun kakkabe ragowar 'yan ta'adda daga yankin mu," a kalaman Buhari. Taron ya samu halartar shugabannin kasashen Chadi, Nijar, da Kamaru. A baya legit.ng ta sanar da ku cewar a yau, Alhamis, ne shugaban kasa Muhammadu Buhari ya tashi zuwa N'Dajamena, babban birnin kasar Chadi, domin shugabantar taron shugabannin kasashen Afrika dake da makwabtaka da tekun Chadi (LBC).

Kamfanin dillancin labarai na kasa (NAN) ta rawaito cewar Buhari ya yi amfani da matsayinsa na shugaban kungiyar kasashen wajen kiran taron domin tattauna yadda za a samu zama zaman lafiya mai dorewa a rukunin kasashen LBC dake fama da hare-haren 'yan ta'addar kungiyar Boko Haram. A wata sanarwa da Femi Adesina, karamin kakakin shugaba Buhari, ya fitar a Abuja ya ce za a yi taron ne yau, Alhamis, a N'Dajamena.

Adesina ya bayyana cewar an gayyaci shugaban kasar Benin zuwa wurin taron saboda kasar sa ta bayar da gudunmawar sojoji domin yakar aiyukan ta'addanci na kungiyar Boko Haram. A cewar Adesina, taron na kwana daya zai tattauna yanayin tsaro a tsakanin kasashen da niyyar samar da hanyoyin da za a bi domin kawo karshen ta'addancin kungiyar Boko Haram.
 

DAGA ISYAKU.COM

Ku biyo mu a Facebook facebook.com/isyakunews

Latsa nan ka shiga group din mu domin samun Labaran mu ta Whatsapp >>> https://chat.whatsapp.com/KIHbQShlAs2GexpIYyxleG

Domin Gyara Wayarka Ka ko FLASHING ka zo SENIORA TECH shago mai lamba 50 hawa na sama, TAUSHI PLAZA, Ahmadu Bello Way Birnin kebbi

Post a Comment

RUBUTA SHARHI KO RA'AYINKA KAN WANNAN LABARI

Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN