Type Here to Get Search Results !

INEC ta fitar da ranar da za a yi zaben Gwamnoni da na yan Majalisa


Legit Hausa

Mahmood Yakubu, shugaban hukumar zabe mai zaman kanta (INEC), ya bayyana cewa zaben yanki a babbar birnin tarayya zai gudana ne a ranar 2 ga watan Maris, 2019, tare da na gwamnoni, da majalisar dokokin jiha. Ya kuma bayyana cewa za’a wallafa jerin sunayen yan takara na zabe a ofishinta na babbar birnin tarayya da kuma yankuna shida a ranar Laraba, 21 ga watan Nuwamba, 2018 (yau).

Yakubu ya bayyana hakan a lokacin ganawa da kwamishinonin zabe a dakin taro na hukumar da ke hedkwatar INEC, Abuja a yau Laraba. Yanzu Yanzu: Za’a yi zaben gwamna, da na majalisar jiha a ranar 2 ga watan Maris - INEC Ya roki jama’a da su duba cikakken bayanai na yan takarar da suke neman wakiltansu.

An kammala zaben fidda gwani na yankunan a ranar 27 ga watan Oktoba 2018, INEC ta bayyana. Bayanan na kunshe ne a wasu rubutu da hukumar INEC din ta wallafa a shafinta na twitter @inecnigeria.
 

DAGA ISYAKU.COM

Shiga shafin mu na Facebook facebook.com/isyakunews

Latsa nan ka shiga group din mu domin samun Labaran mu ta Whatsapp >>> https://chat.whatsapp.com/AlFUDQouyehJRacXxBzbX0

Domin Flashin ko gyaran wayarka Garzaya zuwa SENIORA TECH,shago mai lamba 50, hawa na sama gefen hagu,TAUSHI PLAZA , yamma daga gidan marigayi Waziri Umaru,kan Tiltin Ahmadu Bello, Nassarawa, Birnin kebbi jihar Kebbi. Barka da zuwa gidan sauki wajen gyaran wayar salula a garin Birnin kebbi.

Post a Comment

0 Comments
* Please Don't Spam Here. All the Comments are Reviewed by Admin.

Top Post Ad

Below Post Ad

Shiga group dinmu na WhatsApp domin samun labaran mu kai tsaye LATSA NAN
Domin zama Wakilin mu a garin ku LATSA NAN
Domin aiko Sako/Labari/Korafi LATSA NAN
Domin samun labaran mu a Facebook LATSA NAN
Domin samun labaranmu a Twitter LATSA NAN