'Yan Siyasa 8 da ake zargi da rashawar N232bn kuma suke fafutika akan tazarcen Buhari


Mun samu cewa cikin jiga-jigan 'yan siyasa dake fafutika akan tazarcen shugaban kasa Muhammadu Buhari, a yayin babban zabe da za a gudanar a watan Fabrairun 2019, akwai wasu 8 daga cikin su da ake zargi da laifin rashawa ta kimanin N232bn kamar yadda shafin jaridar The Punch na ranar Asabar ta yau ya bayyana.

Binciken da manema labarai na jaridar suka gudanar ya bayyana cewa, akwai dambarwar wannan zargi tsakanin jiga-jigan 'yan siyasar da kuma hukumomin tsaro musamman hukumar hana yiwa tattalin arziki zagon kasa ta EFCC. Hukumomin tsaron na zargin wannan jiga-jigan 'yan siyasa da aikata laifukan rashawa ta almundahanar dukiyar gwamnati kama daga Naira miliyan dari biyu har zuwa abinda ya kai Naira biliyan dari kan kowanen su.

Wasu daga 'yan siyasar takwas sun kasance mambobi na jam'iyyun adawa musamman ta PDP, inda sauyin shekar su zuwa jam'iyyar APC ya zamto wata tsarkaka tare da katanga tsakanin su da hukumomin tsaro masu gudanar da bincike a kansu.

NAIJ.com ta fahimci cewa, musamman wannan jiga-jigan 'yan siyasa da ake zarginsu da laifin rashawa su na ci gaba da kai ruwa rana tare da fafutika gami da lasar takobbi akan ganin shugaba Buhari ya ci gaba da kasancewa akan karagar mulki har zuwa shekarar 2023.

 Jiga-jigan 'yan siyasar takwas sun hadar da; Sanata mai wakilcin jihar Nasarawa ta Yamma, Abdullahi Adamu, Sanata mai wakilcin jihar Sakkwato ta Arewa kuma tsohon gwamnan jihar; Aliyu Magatakarda Wamakko da kuma tsohon shugaba marar rinjaye a majalisar dattawa kuma tsohon gwamnan jihar Akwa Ibom; Sanata Godswill Akpabio wanda a kwana-kwanan nan ya sauya sheka daga jam'iyyar PDP zuwa APC.

Sauran wadanda ake zargi da kashi a gindinsu sun hadar da; tsohon gwamnan jihar Abia; Orji Uzor Kalu, tsohon sakataren gwamnatin tarayya; Babachir Lawal, gwamnan jihar Zamfara; Abdulaziz Abubakar Yari, tsohon shugaban jam'iyyar PDP na kasa; Ali Modu Sheriff da kuma tsohon gwamnan jihar Ribas kuma Ministan Sufuri; Rotimi Amaechi wanda shine shugaban kungiyar yakin neman zaben shugaba Buhari.
 

Latsa nan ka shiga group din mu domin samun Labaran mu ta Whatsapp >>> whatsapp://chat?code=41x2TuRqdVQ9PrcrucqpTu Shiga cikakken shafin mu kai tsaye www.isyaku.com Tuntube mu ta SMS ko TEXT kawai zuwa 08087645001 ba mu amsa kira

Hausa.naij.ng
Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN