Shugaba Buhari ya bukaci kada yansanda da INEC su sa baki a zaben mutane 2019


Shugaban kasa Muhammadu Buhari ya fadama rundunar yan sandan Najeriya, hukumar zabe mai zaman kanta da sauran hukumomin tsaro a kasar da su bari yan Najeriya su yi zabin ransu a zaben 2019 ba tare da kowani irin barazana ba.

Shugaban kasar ya bayyana cewa shi ma ya amfana daga zaben gaskiya da amana, bayan ya sha kaye sau uku, baya tsoron yin zabe na gaskiya da amana a shekara mai zuwa. Ya sake ba da tabbacin jajircewarsa domin tabbatar da cewa zaben 2019 a karkashin gwamnatinsa ta zamo na gaskiya da amana.

Hakan na zuwa ne a daidai lokacin da Buhari ya nuna rashin jin dadinsa kan yadda kafofin watsa labarai ke rikon lamarin rikicin makiyaya da manoma a kasar sannan ya bayar da shawarar cewa kafofin watsa labarai suyi kokari su nemi sanin tarihin abun Da yake Magana a wani taron tattaunawa day an Najeriya a Beijing, China a jiya Buhari yayi alkawarin cewa yan Najeriya da suka kai matsayin zabe za’a bari su zabi san ransu.

A baya NAIJ.com ta rahoto cewa Buhari ya amince da wasu sabbin nade-nade guda hudu da suke da alaka da kamfanin nan na gwamnatin tarayya dake bugawa tare da tsare takardun sirri watau Nigerian Security Printing and Minting Company. Kamar yadda muka samu, Shugaba Buhari din ya nada Alhaji Abbas Umar Masanawa a matsayin babban manajan Daraktan kamfanin tare kuma da wasu manyan daraktocin sa su biyu.
 

Latsa nan ka shiga group din mu domin samun Labaran mu ta Whatsapp >>> whatsapp://chat?code=41x2TuRqdVQ9PrcrucqpTu Shiga cikakken shafin mu kai tsaye www.isyaku.com Tuntube mu ta SMS ko TEXT kawai zuwa 08087645001 ba mu amsa kira

Hausa.naij.ng
Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN