Mun samu labari cewa rikicin siyasa na nema ta rutsa da
babbar Jam’iyyar adawa ta PDP a wasu Jihohin Arewa. Wadannan Jihohi sun hada da
Kano da kuma Kogi, Sokoto da Jihar Benuwai.
1. Kano A Jihar Kano kun ji labari cewa an fara samun takaddama
tsakanin ‘Yan Kwankwasiyya da kuma manyan PDP a Jihar irin su Malam Ibrahim
Shekarau, Aminu Wali, Bello Hayatu Gwarzo da sauran su. Shekarau da Kwankwaso
su na neman Shugaban kasa
2. Sokoto Da alamu dai PDP za ta shiga rikici a Jihar Sokoto
bayan Gwamnan Jihar Aminu Tambuwal ya sauya sheka. Tambuwal zai samu matsala
wajen takarar Shugaban kasa, sannan kuma akwai rikici tsakanin sa da tsohon
Gwamna Attahiru Dalhatu Bafarawa.
3. Benuwai A Jihar Benuwai ma dai za a buga rikici a 2019.
Gwamna Ortom ya sauya sheka daga APC kwanaki inda yake neman zarcewa a PDP.
Hakan ya kawo rabuwar kai a PDP wanda ya ja har wasu ‘Yan takara su ka fara
komawa Jam’iyyar APC a Jihar.
4. Kogi A Jihar Kogi ana samun rabuwar kai tsakanin ‘Ya ‘Yan
Jam’iyyar PDP. Sanata Dino Melaye na APC ya koma PDP inda zai nemi Jam’iyyar ta
basa tikitin sake tsayawa kujerar Sanata a Jihar. Sai dai hakan na neman kawo
rikici a Jam’iyyar adawar a Kogi.
Latsa nan ka shiga group din mu domin samun Labaran mu ta Whatsapp >>> whatsapp://chat?code=41x2TuRqdVQ9PrcrucqpTu Shiga cikakken shafin mu kai tsaye www.isyaku.com Tuntube mu ta SMS ko TEXT kawai zuwa 08087645001 ba mu amsa kira
Hausa.naij.ng