Type Here to Get Search Results !

Babu wani tantancewa da za’a yiwa Saraki, Atiku, Kwankwaso da sauransu a yanzu


Baya ga yan takarar kujerar shugaban kasa, jam’iyyar bata ambaci wani kwamiti da zai yi duba ga takardun sauran yan jam’iyya. Tuni dai yan takara da dama sun yanki fam din takarar shugabancin kasa a karkashin jam’iyyar inda suke jira a kaddamar da kwamitin.

Daga cikin yan takaran da suka yanki fam dinsu sun hada da tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar, tsohon gwamnan jihar Kano, Sanata Rabiu Kwankwaso, Gwamnan jihar Sokoto, Aminu Tambuwal, da kuma gwamnan jihar Gombe, Ibrahim Dankwambo. Har ila yau akwai tsohon gwamnan jihar Jigawa, Alhaji Sule Lamido, tsohon ministan ayyuka na musamman, Alhaji Tanimu Turaki; tsohon gwamnan jihar Kano, Ibrahim Shekarau; Attahiru Bafarawa da kuma Dr Ahmed Datti.

Babban sakataren labaran jam’iyyar, Mista Kola Ologbondiyan, ya fadama majiyarmu cewa a ranar Lahadi cewa babu laifi a cikin jinkirtawan, cewa jam’iyyar zata gabatar da mambobin kwamitin ba da dadewa ba. Ya bayyana cewa jam’iyyar ta mayar da hankali wajen siyar da fam dinta, cewa da zaran an kammala da wannan kwamitin masu ruwa da tsaki zata saki sunaye.

A wani lamari na daban, mun ji cewa alkalin alkalai kuma ministan shari’a, Mista Abubakar Malami ya kalubalanci hukuncin babban kotun tarayya na sauraron karar dake bukatar a dakatar da tsige Dr Bukola Saraki a matsayin shugaban majalisar dattawa. Ministan shari’an ya bukaci babban kotun da tayi watsi da karar da tsoffin sanatocin jam’iyyar All Progressives Congress (APC), Rafiu Adebayo da Isa Misau suka shigar a gabanta.
 

Latsa nan ka shiga group din mu domin samun Labaran mu ta Whatsapp >>> whatsapp://chat?code=41x2TuRqdVQ9PrcrucqpTu Shiga cikakken shafin mu kai tsaye www.isyaku.com Tuntube mu ta SMS ko TEXT kawai zuwa 08087645001 ba mu amsa kira

Hausa.naij.ng

Top Post Ad

Below Post Ad

Shiga group dinmu na WhatsApp domin samun labaran mu kai tsaye LATSA NAN
Domin zama Wakilin mu a garin ku LATSA NAN
Domin aiko Sako/Labari/Korafi LATSA NAN
Domin samun labaran mu a Facebook LATSA NAN
Domin samun labaranmu a Twitter LATSA NAN