Type Here to Get Search Results !

Main event

Majalisa ta fara gyaran dokar zabe da Buhari ya yi watsi da ita sau 2


Majalisar tarayya ta fara aikin kan kudirin yin garambawul ga dokar zabe na 2010 da shugaba Muhammadu Buhari ya ki saka hannu a kai saboda wasu matsaloli da ya ke son majalisar ta gyra.

Mambobin majalisar dattawa da na wakilai na kwamitin gyarar dokar zaben ne suka bayar da sanarwan a yau Litinin a Abuja inda suka ce kwamitin ta fara zama domin duba dalilan da yasa shugaba Buhari ya ki amincewa da kudirin domin su gyara.

A lokacin da ya ke magana da manema labarai kafin kwamitin ta shiga taron ta, Ciyaman din kwamitin INEC a majalisa, Sanata Suleiman Nazifi ya ce kwamitin na da babban nauyi a kanta saboda dukkan 'yan Najeriya sun sanya musu ido.

Nazif ya kuma ce wannan shine karo na hudu kwamitin za tayi aiki kan kudirin dokan wanda shugaba Buhari ya mayarwa majalisar har sau biyu. "Nayi imanin cewa aikin da mu keyi zai amfani 'yan Najeriya, Inji Nazif. Shugaba Buhari ya aike wasika ga shugaban majalisar dattawa, Bukola Saraki da Kakakin majalisar wakilai, Yakubu Dogara domin sanar da matsayarsa na kin amincewa da dokar.
 

Latsa nan ka shiga group din mu domin samun Labaran mu ta Whatsapp >>> https://chat.whatsapp.com/AlFUDQouyehJRacXxBzbX0 Shiga cikakken shafin mu kai tsaye www.isyaku.com Tuntube mu ta SMS ko TEXT kawai zuwa 08087645001 ba mu amsa kira

Hausa.naija.ng

Post a Comment

0 Comments
* Please Don't Spam Here. All the Comments are Reviewed by Admin.

Top Post Ad

Below Post Ad

Shiga group dinmu na WhatsApp domin samun labaran mu kai tsaye LATSA NAN
Domin zama Wakilin mu a garin ku LATSA NAN
Domin aiko Sako/Labari/Korafi LATSA NAN
Domin samun labaran mu a Facebook LATSA NAN
Domin samun labaranmu a Twitter LATSA NAN

Hollywood Movies