Type Here to Get Search Results !

Kansilolin karamar hukumar Yauri a jihar Kebbi sun ce sun tsige shugaban karamar hukumar

isyaku.com | 25-9-2018 |

Hotunan wasu takardu da muka samu daga garin Yauri na jihar Kebbi, sun nuna cewa Kansiloli goma na karamar hukumar sun saka hannu a wata takarda da ke nuna cewa sun tsige shugaban karamar hukumar Yauri a ranar 25 ga watan Satumba 2018.

Kansilolin sun rubuta cewa shugaban Karamar hukumar Yauri ya kasa gabatar da kansa a wani komiti da aka kafa domin ya kare kanshi bisa zargi da ake yi masa, amma daga bisani wani hadiminsa ya zo yace masu suna da aiki a gabansu daga bisani ya tafi abinsa.

Takardar ta ce, sakamkon haka ne Kansilolin da suka zayyana sunayensu a takardar suka tsige shugaban karamar hukumar duk da yake ba inda aka ambaci sunans shugaban karamar hukumar ta Yauri a cikin takardar.

Hakazalika takardar ta ce ofishin shugaban karamar hukumar na nan a rufe kuma jami'an tsaro suna bayar da tsaro a wajen.

Yunkurin mu na jin ta bakin kakakin hukumar yansanda na jihar Kebbi ya ci tura, domin dai bai mayar da martani a sakon SMS da muka tura masa ba, hakazalika bai amsa kiraye-kirayen wayar Salula da muka yi masa ba kafin lokacin rubuta wannan rahotu.

A bangaren shugaban karamar hukumar ta Yauri da jagoran Kansiloli da suka ce sun tsige shugaban karamar hukumar , su ma bamu same su ba a wayar Salula domin tantance lamarin.

Latsa nan ka shiga group din mu domin samun Labaran mu ta Whatsapp >>> https://chat.whatsapp.com/AlFUDQouyehJRacXxBzbX0 Shiga cikakken shafin mu kai tsaye www.isyaku.com Tuntube mu ta SMS ko TEXT kawai zuwa 08087645001 ba mu amsa kira

Post a Comment

0 Comments
* Please Don't Spam Here. All the Comments are Reviewed by Admin.

Top Post Ad

Below Post Ad

Shiga group dinmu na WhatsApp domin samun labaran mu kai tsaye LATSA NAN
Domin zama Wakilin mu a garin ku LATSA NAN
Domin aiko Sako/Labari/Korafi LATSA NAN
Domin samun labaran mu a Facebook LATSA NAN
Domin samun labaranmu a Twitter LATSA NAN