APC ta karyata rahoton EIU, HSBC na cewar tattalin arziki zai karye idan Buhari ya zarce


Jam'iyyar APC ta karyata rahotan sashen kwararru kan tattalin arzikin kasa (EIU) da HASBC, wani kamfani mai harkoki a kasashe kan bankuna da kudade, rahoton da ke cewa zarcewar shugaban kasa Muhammadu Buhari a 2019 zai jawo mummunan karyewar tattalin arzikin Nigeria.

A cikin wata sanarwa da ta bayar a ranar Laraba, dauke da sa hannun Yekini Nabena, Sakataren watsa labarai na jam'iyyar na kasa, APC ta ce rahoton da kamfanin EIU ya fitar, na nuni da cewa jam'iyyar adawa ta PDP ce zata lashe zaben 2019, da cewar gwamnatin gaba zata fuskanci babbar matsalar tsaro. "Gwamnatin gaba zata fuskanci karyewar tattalin arzikin kasa (bayan zaben 2019) wanda hakan ke nuni da cewa barazanar da tsaro ke fuskanta a kasar zai zarce na yanzu" a cewar rahoton EIU.

Haka zalika rahoton ya bayyana cewa: "Muna kyautata tsammanin samun karuwar matsalolin tsaro, ko da ya ke rundunar soji kwararru ne a wannan bangaren" Jam'iyyar APC ta bukaci yan Nigeria da su kauracewa wannan "hasashe da rahoton kamfanin" domin sanin su da kuma watsi da su kasancewar ba su ne na farko da suka taba yin irin wannan hasashe ba, a shekarun baya hukumomin kasashen turai sun sha fitar da irin wadannan rahotanni.

A shekarun baya, an fitar da rahotannin cewa kasar Nigeria zata wargaje a 2015, biyo bayan ballewar wasu kabilu da zasu bukaci samun yancin cin gashin kansu. Sai dai, an doshi akalla shekaru 4 da wucewar shekarar da akayi hasashen zata zamo shekarar rabuwar Nigeria, mai-makon ma kasar ta rabu, sai ma kara dunkulewa da ta ke yi, yayin da gwamnatin shugaban kasa Muhammadu Buhari ta maida hankali wajen samar da hadin kai a cikin kasar.

APC ta buga misali da gwamnatocin baya da suka gabata, wadanda aka saci kudaden jama'a, gwamnatocin da suka mayar da wasu hukumomi kamar karnukan farautarsu, irin su hukumar jarabawar share fagen shiga manyan makarantu (JAMB), hukumar tattara haraji ta kasa (FIRS) da kuma hukumar hana fasa kwabri ta kasa (NCS). Jam'iyyar ta kuma bayyana takaicinta na yadda EIU ta ki lura da irin kudaden da aka kwato daga barayin gwamnati, ta hanyar hukumar EFCC.
 

Latsa nan ka shiga group din mu domin samun Labaran mu ta Whatsapp >>> whatsapp://chat?code=41x2TuRqdVQ9PrcrucqpTu Shiga cikakken shafin mu kai tsaye www.isyaku.com Tuntube mu ta SMS ko TEXT kawai zuwa 08087645001 ba mu amsa kira

Hausa.naij.ng

Post a Comment

RUBUTA SHARHI KO RA'AYINKA KAN WANNAN LABARI

Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN