Duba adadin yawan mutane da aka kashe a jihara Zamfara daga 2011 zuwa yau


Gwamna Abdulazeez Yari ya bayyana cewa daga 2011 kawo yanzu an kashe mutane sama da 2000 a cikin Jihar Zamfara. Gwamnan ya bada adadin wadanda aka hallaka a Jihar ne a makon nan.

 Abdulaziz Yari ya tabbatar da cewa mutum sama da 2, 300 aka rasa cikin shekaru kusan 8 da yayi yana mulki Jihar Zamfara. Gwamnan ya bayyana wannan ne wajen wani taro da Gwamnati ta shirya da al’ummar Jihar a cikin Garin Gusau. Ministan yada labarai Lai Mohammed da kuma Ministocin tsaro da na harkar ruwa watau Mansur Dan-Ali da Suleiman Adamu sun halarci taron.

Yari yace rikicin ya jawo an samu ja-baya kwarai da gaske wajen harkar noma a Jihar Zamfara. Gwamnan ya kuma sanar da cewa an rasa tumaki fiye da 25, 000 daga lokacin da rikici ya barke a Zamfara kawo yanzu. Yari ya nuna takaicin sa ganin cewa kusan kaf mutanen Zamfara Musulmai ne amma ake samun irin wannan kashe-kashe.

Gwamna Yari yace a 2014, kaf Jihar Zamfara Sojoji ba su wuce 24 inda shi kuma Ministan labarai ya nuna cewa an fara samun saukin rikici a Yankin. Ministan tsaro na kasar ya nemi jama’a su daina fadawa masu tada rikicin asirin Jami’an tsaro.

Kwanaki kun ji cewa wani Tsohon ‘Dan Majalisar Wakilan Tarayyar Najeriya yace akwai rikici shigen irin na ‘Yan ta’addan Boko Haram a Zamfara wanda yayi kira da Gwamnati ta dauki mataki.
 

Latsa nan ka shiga group din mu domin samun Labaran mu ta Whatsapp >>> whatsapp://chat?code=41x2TuRqdVQ9PrcrucqpTu Shiga cikakken shafin mu kai tsaye www.isyaku.com Tuntube mu ta SMS ko TEXT kawai zuwa 08087645001 ba mu amsa kira

Hausa.naij.ng

Post a Comment

RUBUTA SHARHI KO RA'AYINKA KAN WANNAN LABARI

Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN