Yadda dan makaranta ya kashe mutum 3 bayan ya shiga kungiyar asiri


Jami’an yan sandan dake yaki da fashi da makami a jihar Imo sun kama wani gawurtaccen dan kungiyar asiri kuma makashi, Chijioke Ogbonna wadda aka fi sani da Ogotiti. Yayinda yan sanda suka gurfanar da shi a ranar Asabar da ya gaata, Ogotiti ya fadama manema labarai cewa ya kashe mutane uku tunda ya shiga kungiyar asiri a shekarar 2014. Matashin mai shekaru 23 wanda ya kasance dan makarantar Federal Polytechnic, Nekede, yace kudirin da ya dauka na daukar fansa ne ya kai shi ga kashe mutane uku, daya daga cikinsu ya kasance dan kungiyar adawarsu.

Ogbotiti wadda ya kasance dan asalin garin Umuejije, karamar hukumar Isialangwa ta kudu dake jihar Abia yayi bayanin cewa babban makami da yake amfani da shi ya kasance bindigar gargajiya.

Jami’in hulda da jama’a na rundunaar yan sandan jihar Imo, Andrew Enwerem ya bayyana mai laifin a matsayin gawurtaccen dan kungiyar asiri da fashi da makami, ya kara da cewa jami’an SARS ne suka kama shi a ranar 19 ga watan Agusta a Ama-Hausa dake yankin Owerri, babban birnin jihar. Enwerem yace yan sanda na neman mai laifin tun a 2014 kan zargin rawar ganin da yake takawa wajen aikata ayyukan laifi.
 

Latsa nan ka shiga group din mu domin samun Labaran mu ta Whatsapp >>> whatsapp://chat?code=41x2TuRqdVQ9PrcrucqpTu Shiga cikakken shafin mu kai tsaye www.isyaku.com Tuntube mu ta SMS ko TEXT kawai zuwa 08087645001 ba mu amsa kira

Hausa.naij.ng
Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN