Dan daban siyasa da ya tsere daga hannun SARS ya gamu da ajalinsa a rikicin siyasa

Rahotanni sun nuna cewa mutum 3 ne suka mutu a wani tashin hankali tsakanin magoya bayan jam'iyar APC da PDP a yankin Brass da ke jihar Bayelsa makonni uku da suka gabata.

Wasu sabbin bayanai sun ce daya daga cikin wadanda aka kashe a wannan tashin hankalin Kelly Ikurusi, yana cikin jerin sunayen mutanen da rundunar yansanda ta jihar Bayelsa ke nema ruwa jallo sakamakon ballewa daga dakin da aka tsare su a sashen SARS na rundunar 7 ga watan Nuwamba 2017.

Bayanai daga yansandan jihar sun ce mutum 10 ne suka tsere daga hannun rundunar wadanda suke fuskantar bincike da suka shafi manyan laifuka har da fashi da makami.

Latsa nan ka shiga group din mu domin samun Labaran mu ta Whatsapp >>> whatsapp://chat?code=41x2TuRqdVQ9PrcrucqpTu Shiga cikakken shafin mu kai tsaye www.isyaku.com Tuntube mu ta SMS ko TEXT kawai zuwa 08087645001 ba mu amsa kira
Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN