Type Here to Get Search Results !

Ficewar Saraki daga jam’iyyar APC tamkar mutuwar jam’iyyar ne ― Balarabe Musa


Tsohon gwamnan jihar Kaduna Alhaji Balarabe Musa ya bayyana cewa ficewar shugaban majalisar dattawa Dakta Abubakar Bukola Saraki daga jam’iyyar APC zuwa jam’iyyar PDP zai kawo nakasu ga nasarar shugaba Muhamm ad Buhari a kakar zaben shekarar 2019.

Tsohon gwamnan ya bayyana hakan ne a cikin wata ganawa da ya yi da manema labarai a jiya Talata, inda ya jaddada cewa babu shakka ficewar Sarakin za ta kawo tangarda tare da kawo cikas ga shugaba Muhammad Buhari tare da jam’iyyarsa ta APC a zaben 2019. Idan za'a iya tunawa dai a ranar Talata ne dai shugaban majalisar dattawan ya fice daga jamiyyar APC zuwa jam’iyyar APC zuwa jam’iyyar PDP.

"Ficewar Bukola Saraki daga jam’iyyar APC ya sanya jam’iyyar cikin rudani, domin kai tsaye karshen jam’iyyar ya zo". A cewar Balarabe Musa. Sannan ya kara da "Babu Shakka abubuwan da za su biyo baya bayan ficewar Saraki daga jam’iyyar APC, ba zai haifarwa da jam’iyyar da mai ido ba. Domin zai kawo cikas ga nasarar jam’iyyar a zabe mai zuwa".
 

Latsa nan ka shiga group din mu domin samun Labaran mu ta Whatsapp >>> whatsapp://chat?code=41x2TuRqdVQ9PrcrucqpTu Latsa nan domin ka sauke Manhajarmu ISYAKU.APK https://docs.google.com/uc?export=download&id=0B7lmLLhGZSx5OTVENFlsTkllRTQ Shiga cikakken shafin mu kai tsaye www.isyaku.com Tuntube mu ta SMS ko TEXT kawai zuwa 08087645001 ba mu amsa kira

Hausa.naij.ng

Top Post Ad

Below Post Ad

Shiga group dinmu na WhatsApp domin samun labaran mu kai tsaye LATSA NAN
Domin zama Wakilin mu a garin ku LATSA NAN
Domin aiko Sako/Labari/Korafi LATSA NAN
Domin samun labaran mu a Facebook LATSA NAN
Domin samun labaranmu a Twitter LATSA NAN