2019: Akwai gwamnonin PDP 4 dake yiwa APC aiki ta karkashin kasa - Kofa


Abdulmumin Jibrin Kofa, dan majalisar wakilai mai wakiltar kananan hukumomi Kiru da Bebeji a jihar Kano, ya yi ikirarin cewar akwai gwamnonin jam'iyyar PDP 4 dake aiki tare da jam'iyyar APC domin ta kai ga nasara a zaben 2019. Duk da bai ambaci sunayen gwamnonin ba, Kofa ya bayyana cewar akwai yarjejeniya tsakaninsu da jam'iyyar APC. Da yake ganawa da manema labarai a Abuja a jiya, Laraba, Kofa ya ce, "a halin yanzu akwai gwamnonin jam'iyyar PDP 4 zuwa 5 da aka kulla yarjejeniyar goyon bayan takarar shugaba Buhari da su a zaben shugaban kasa."

Sannan ya kara da cewa, "jam'iyyar APC ba ta girgiza ba saboda fitar wasu 'ya'yanta ba." Kazalika ya kara da cewar APC na daukan matakan ganin cewar ta cigaba da juya siyasar jihohin da take da yawan magoya baya.

"Da a ce wani dan takarar APC ta tsayar ba shugaba Buhari ba, da sai na dan ji raina ya sosu saboda ficewar wasu 'ya'yan jam'iyyar amma yanzu bana jin ko dar a raina saboda shugaba Buhari ke yiwa APC takarar shugaban kasa. "Duk masu sukar Buhari da canja sheka 'yan siyasa ne da basu da wasu jama'a, a saboda haka zaben 2019 zai kasance ne tsakanin 'yan Najeriya da wasu tsirarun 'yan siyasa masu son zuciya," in ji Kofa.
 

Latsa nan ka shiga group din mu domin samun Labaran mu ta Whatsapp >>> whatsapp://chat?code=41x2TuRqdVQ9PrcrucqpTu Latsa nan domin ka sauke Manhajarmu ISYAKU.APK https://docs.google.com/uc?export=download&id=0B7lmLLhGZSx5OTVENFlsTkllRTQ Shiga cikakken shafin mu kai tsaye www.isyaku.com Tuntube mu ta SMS ko TEXT kawai zuwa 08087645001 ba mu amsa kira

Hausa.naij.ng
Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN