Kotu ta zartar da hukuncin kisa ga dansanda da ya harbe wani dan acaba

Wata babbar Kotu a garin Ilaro na jihar Ogun, ta yanke ma wani jami'in dansanda mai suna kofur Moruf Awoleke , mai lambar dansanda 389719 hukuncin kisa bayan ta kama shi da laifin kashe wani dan'acaba mai suna Akanji Ahmed.

A 2016 ne dan acaban ya gamu da ajalinsa a hannun wannan dansanda, bayan wata gajeruwar gardama sakamakon kamashi a kan babur bayan karfe 9 na dare, sakamakon wani umarni da kwamishinan yansanda ya bayar a wancan lokaci na hana yin acaba bayan karfe 9 na dare.

Amma bayan yansandan sun yi kokarin wucewa da babur ne, sai cacan bakin ya zafafa da ya sa kofur Moruf ya harbe Akanji.Sakamakon haka ya mutu.

Wannan lamari ya faru a garin Ilaro hedikwatar karamar hukumar Yewa ta kudu a jihar Ogun.

Alkalin Kotun ya zartar da hukuncin kisa ne, bayan ya ce Kotu ta gamsu da hujjoji da masu gabatar da kara suka shigar, wanda a cewarsa, hujjoji ne da ke fayyace a kowani mataki.

Latsa nan ka shiga group din mu domin samun Labaran mu ta Whatsapp >>> https://chat.whatsapp.com/Lq4Z5kPck53Le3ibU9RUnY Shiga cikakken shafin mu kai tsaye www.isyaku.com Tuntube mu ta SMS ko TEXT kawai zuwa 08087645001 ba mu amsa kira
Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN