Idan na bukaci majalisar dokoki su tsige Buhari, za su yi – Galadima


Buba Galadima, shugaban kungiyar sabuwar APC, yace kungiyar ta fi yawan mutane a majalisar dokoki da za su tsige shugaban kasa Muhammadu Buhari. A cewar jaridar Thisday, Galadima ya bayyana hakan ne yayinda yake maida martani ga Adams Oshiomhole wanda ya bayyana R-APC a matsayin harsuna yan baranda. Oshiomhole ya bayyana hakan ne bayan tattaunawar da yayi da masu ruwa da tsaki na APC a majalisar wakilai

A baya NAIJ.com ta rahoto cewa matasa a Kano karkashin wata kungiyar siyasa mai suna ‘Ranar Wanka Buhari/Ganduje Progressive Group’, sun kammala shirye-shirye don yin gangamin matasa miliyan uku a jihar domin nuna hamayya da ayyukan siyasa na gammayar kugiyar da sabuwar APC wato Reformed APC (R-APC). Da yake zantawa da manema labarai a Kano a ranar Alhamis, shugaban kungiyar, Alhaji Bala Salihu Dawaki, ya ce kwanan nan za su gudanar da tattakin, a cewarsa, an kammala shirye-shirye.
 

Latsa nan ka shiga group din mu domin samun Labaran mu ta Whatsapp >>>

 https://chat.whatsapp.com/Lq4Z5kPck53Le3ibU9RUnY

Shiga cikakken shafin mu kai tsaye www.isyaku.com

Tuntube mu ta SMS ko TEXT kawai zuwa 08087645001 ba mu amsa kira

hausa.naij.ng
Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN