Alakwurra 3 da Buhari ya dauka a 2015 kuma har yanzu bai cika su ba


Kamar kowane dan siyasa, Shugaba Muhammadu Buhari a lokacin yakin neman zabe a shekarar 2015 ya zagaya jahohin Najeriya tare da kuma ganawa da daruruwan kungiyoyi inda ya yi masu alkawurra da dama idan dai har suka zabe shi.

Duk da dai siyasa daman kamar yadda masu fashin baki da dama kan fada cewa ta gajin rashin cika alkawari, amma talakawan Najeriya da ma al'ummomin kasashen duniya sun yi ammanar cewa shugaba Buhari ya sha ban-ban da sauran 'yan siyasa.

1. Magance rashin tsaro: 

Duk da dai a iya cewa gwamnatin sa ta samu nasara sosai musamman ma a yakin da take yi da 'yan kungiyar Boko Haram, har yanzu akwai sauran rina a kaba a sassan kasar. 

2. Farfado da tattalin arzki: 

Da samun karayar darajar kudin naira tare kuma da hauhawar farashin kayan masarufi da na abinci, masana da dama na ganin yanzu tattalin arzikin Najeriya kara tabarbarewa yayi. 

3. Samar da aikin yi ga matasa: 

Duba da irin shire-shiren da gwamnatin ta bullo da su da ke da alaka ta kai tsaye ga samarwa matasa aikin yi kamar su shirin nan na N-power da kuma harkar noma, a iya cewa gwamnatin ta kokarta. Amma dai saboda yawan al'ummar kasar, har yanzu rashin aikin yi a tsakanin matasa na nan ba'a magance shi ba.
 

Latsa nan ka shiga group din mu domin samun Labaran mu ta Whatsapp >>> whatsapp://chat?code=41x2TuRqdVQ9PrcrucqpTu Latsa nan domin ka sauke Manhajarmu ISYAKU.APK https://docs.google.com/uc?export=download&id=0B7lmLLhGZSx5OTVENFlsTkllRTQ Shiga cikakken shafin mu kai tsaye www.isyaku.com Tuntube mu ta SMS ko TEXT kawai zuwa 08087645001 ba mu amsa kira

Hausa.naij.ng
Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN