Wani Mutum ya Kashe Kansa a Masallacin Harami na Birnin Makkah


Cikin wani rahoto mai kunshe da ban al'ajabi ya bayyana cewa, wani matashin mutum ya kashe kansa yayin da ya jefo kansa tun daga saman bene na kololuwa dake babban Masallaci mai alfarma na Birnin Makkah a can Kasar Saudiyya. 

Hukumomin tsaro na Kasar Saudiyya sun bayyana cewa, wannan matashin mutum da ya ziyarci kasa mai tsarki domin gudanar da aikin Umarah a wannan wata na Ramadana ya mutu ne nan take yayin da ya fado kasa da misalin karfe 9.20 na daren ranar Juma'ar da ta gabata. 

Rahotanni sun bayyana cewa, wannan matashi bai wuci shekaru 26 a duniya ba kuma dan asalin kasar Faransa ne da ya yi tsarki na shiga addinin Islama kamar yadda wata jarida ta kasar Taki, Daily Sabah ta bayyana. 


kamar yadda jaridar The Punch ta ruwaito, wannan ba shine karo na farko da wani mahaluki ya yi yunkurin kashe kansa a harabar Masallaci mai Alfarma daura da Dakin Ka'aba duk da cewar kisan kai a addinin Islama yana daya daga cikin manyan laifuka na kololuwa da ba bu yafiya ga duk wanda ya aikata hakan.

An garzaya da gawar wannan Matashi zuwa asibiti domin binkicen dalilin da ya sanya ya yankewa kansa wannan mummunan hukunci tare da binciken yadda ya aikata hakan. 

A shekarar da ta gabata ne wani mutum dan kasar ta Saudiyya ya yukurin kashe kansa ta hanyar bankawa kansa wuta a gaban dakin Ka'aba yayin da jami'an tsaro suka yi gaggawar hana shi.
 

Don samun labaranmu ta Whatsapp ka rubuto YES a SMS zuwa 08087645001. Shiga cikakken shafinmu. www.isyaku.com 

#hausa.naij.com

Post a Comment

RUBUTA SHARHI KO RA'AYINKA KAN WANNAN LABARI

Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN