A
Morocco wasu gungun matasa sun lakada wa wata daliba mai kimanin
shekaru 20 da haifuwa duka da kulakai,sakamakon tuhumar ta da suke da
yin zina a watan Ramadan.
A yanzu haka bidiyon wannan lamarin ya gama duniya,inda kowa ke ci gaba da fadar albarkacin bakinsa.
Bidiyon na nuna fuskokin wasu fusatattun matasa wadanda suka far wata matashiya wacce ke zaune da wani tsoho a wata mota.
Matashiyar ta yi kokarin fada musu cewa, ita daliba ce,kuma tsohon da ke tare da ita, direba ne.
Amma
ba su bar ta karasa ba,inda nan take suka far ma ta,yayin da
jama'ar unguwa kuma, suka mara musu baya ta hanyar jifar yarinyar,suna
cewa
"Zina a wata mai tsarki, ba ki ji kunya ba".
Wannan lamarin yayi matukar tayar da hankalin al'umar ciki da wajen kasar Morocco.
#TRT