Sama ko kasa, an nemi alkalin da zai shari’ar El-Zakzaky an rasa


Rashin bayyanar mai shari’a Gideon Kurada domin sauraren shari’ar shugaban mabiya mazabar Shi’a El-Zakzaky da matarsa da ya gamu da cikas a dalilin rashin bayyanar alkalin 

Gwamnatin jihar Kaduna dai ta zayyana laifuka takwas da take tuhumar Ibrahim El-Zakzaky da matar shugaban mabiya Shi’an na Najeriya. Daga cikin laifukan da ake zarginsu da shi sun hada da hada baki wajen kulla kitsattsiya da kin yin katabus gami da tabuka komai wajen kare faruwar rasa rayukan mutane da sauransu. 

Amma sai dai an hana ‘yan jarida shiga cikin harabar kotun domin shaida yadda zaman kotun zai kasance. Lauyan wanda ake kara (Zakzaky) Femi Falana (SAN), ya shaidawa kamfanin dillancin labarai na kasa (NAN) cewa, alkalin yana sane ya ki halartar kotun domin sauraren shari’ar A saboda haka ne lauyan wanda ake kara da kuma lauyan mai karewa sun cimma matsayar dage zaman zuwa 11 ga watan Yuli domin cigaba da shari’ar. 

Falana ya kuma nuna ganin baiken jami’an ‘yan sanda na dakatar da ‘yan jarida daga shiga kotun domin ganin yadda zaman zai kaya, domin kuwa a cewarsa babu wata doka da ta hana mutane shaida zaman kowacce shari’a.
 
Don samun labaranmu ta Whatsapp ka rubuto YES a SMS zuwa 08087645001. Shiga cikakken shafinmu. www.isyaku.com 

hausa.naij.ng
Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN