Neman budurwa daya ya sanya wani mutum cinnawa dayan wuta


Tun da farko a cewar Muhammed ya gargadi Usman da hawainiyarsa ta kiyayi ramar matar da zai aura don kuwa har yayi tambaya amma Usman din yaki ji balle ya saurara. Sannan ya bayyanawa ‘yan sanda cewa ya dauki matakin ne domin yayi duk mai yiwuwa don ganin usman din ya kyale masa matar da yake mutukar son aura, kuma ko kusa ba ya nadamar wannan aika-aika da yayi. 

“Ba na nadamar abinda na aikata saboda inda ban kashe shi a lokacin ba da ni zai kashe, gara ya tafi can don kar ma ya sake hada hanya da ni” “Ban yi aure ba, kuma ban damu da duk matakin da zai biyo baya ba, abu mai muhimmanci kawai shi ne nayi maganinsa daga shiga sabga ta. Akwai mata da yawa amma sai ya zabi ya cigaba da neman matar da na riga da nayi tambayar aurenta, hukuncin da na dauka shi ne ya dace da shi”. Baba ya jaddada.

Kakakin rundunar ‘yan sanda na jihar Muhammad Abubakar ya bayyana cewa wanda ake zargin ya aika wani yaro ne mai suna Abdul ya siyo masa kwalba uku na fetir wanda yayi amfani da shi wajen babbaka abokin neman budurwar tasa. Abubakar ya ce anyi sauri an garzaya da wanda iftila’in ya faru da shi cibiyar kula da lafiya ta tarayya (FMC) dake 

Bida daga basani kuma aka mayar da shi zuwa asibitin Gwagwalada na Abuja inda ya cigaba da karbar magani kafin daga bisani rai yayi halinsa. Kuma za’a kai maganar gaban alkali da zarar an kammala bincike.
 
Don samun labaranmu ta Whatsapp ka rubuto YES a SMS zuwa 08087645001. Shiga cikakken shafinmu. www.isyaku.com

hausa.naij.ng
Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN