Type Here to Get Search Results !

Main event

Yan sanda sun damke yan Shi’a 42 masu alaka da kisan dan sanda a Kaduna


Hukumar yan sandan Najeriya a jihar Kaduna ta damke mambobin kungiyar Shi’a 42 tattare da kisan wani jami’in dan sanda a jiya Alhamis, 21 ga watan Yuni a jihar Kaduna. 

Kakakin hukumar yan sanda, Mukhtar Aliyu, ya bayyana wannan kamu ne a yau Juma’a, 22 ga watan Yuni a jihar Kaduna. Ya ce lallai za’a gurfanar da wadannan mutane 42 muddin an kammala bincike a kan su. Damke wadannan yan Shi’a ya faru ne bayan rikici ya barke tsakanin jami’an yan sanda da yan kungiyar Shi’a masu zanga-zangar cigaba da tsare shugabansu kuma malaminsu, Sheik Ibrahim Zakzaky 

NAIJ.com ta kawo muku rahoton cewa an hallaka dan sanda daya har lahira a sabuwar rikici da ya barke tsakanin yan sanda da yan kungiyar Shi'a a zanga-zangan da sukeyi kan cigaba da tsare shugabansu, Sheik Ibrahim Zakzaky. Kakakin hukumar yan sanda a jihar Kaduna, Muktar Aliyu, ya tabbatar da wannan labari da ya faru a yau Alhamis, 1 ga watan Yuni 2018. 

Game da cewarsa, dan sandan na tafiyarsa a kan hanya kawai sai yyan Shi'an sukayi masa ribiti da caccaka masa wuka har lahira. Sheikh Ibrahim El-Zakzaky dai yana gurfana a kotu ne kan laifin tara mabiya ba bisa doka ba, kokarin fito-na-fito da gwamnati.
 

Don samun labaranmu ta Whatsapp ka rubuto YES a SMS zuwa 08087645001. Shiga cikakken shafinmu. www.isyaku.com

hausa.naij.ng

Top Post Ad

Below Post Ad

Shiga group dinmu na WhatsApp domin samun labaran mu kai tsaye LATSA NAN
Domin zama Wakilin mu a garin ku LATSA NAN
Domin aiko Sako/Labari/Korafi LATSA NAN
Domin samun labaran mu a Facebook LATSA NAN
Domin samun labaranmu a Twitter LATSA NAN

Hollywood Movies