Hukumar yan sandan Najeriya a jihar Kaduna ta damke mambobin
kungiyar Shi’a 42 tattare da kisan wani jami’in dan sanda a jiya Alhamis, 21 ga
watan Yuni a jihar Kaduna.
Kakakin hukumar yan sanda, Mukhtar Aliyu, ya bayyana wannan
kamu ne a yau Juma’a, 22 ga watan Yuni a jihar Kaduna. Ya ce lallai za’a
gurfanar da wadannan mutane 42 muddin an kammala bincike a kan su. Damke wadannan
yan Shi’a ya faru ne bayan rikici ya barke tsakanin jami’an yan sanda da yan
kungiyar Shi’a masu zanga-zangar cigaba da tsare shugabansu kuma malaminsu,
Sheik Ibrahim Zakzaky
NAIJ.com ta kawo muku rahoton cewa an hallaka dan sanda daya
har lahira a sabuwar rikici da ya barke tsakanin yan sanda da yan kungiyar
Shi'a a zanga-zangan da sukeyi kan cigaba da tsare shugabansu, Sheik Ibrahim
Zakzaky. Kakakin hukumar yan sanda a jihar Kaduna, Muktar Aliyu, ya tabbatar da
wannan labari da ya faru a yau Alhamis, 1 ga watan Yuni 2018.
Game da cewarsa,
dan sandan na tafiyarsa a kan hanya kawai sai yyan Shi'an sukayi masa ribiti da
caccaka masa wuka har lahira. Sheikh Ibrahim El-Zakzaky dai yana gurfana a kotu
ne kan laifin tara mabiya ba bisa doka ba, kokarin fito-na-fito da gwamnati.
Don samun labaranmu ta Whatsapp ka rubuto YES a SMS zuwa 08087645001. Shiga cikakken shafinmu. www.isyaku.com
hausa.naij.ng