Magidanci da iyalansa hudu sun mutu a Ogun

Rundunar 'yan sanda a jihar Ogun da ke kudancin Najeriya ta tabattar da mutuwar wani magidanci da matarsa da kuma 'ya'yansa uku bayan sun tare a sabon gidansu da ke garin Sagamu.

Kakakin rundunar 'yan sanda a jihar ya shaida wa BBC ewa kawo yanzu ana gudanar da bincike kan lamarin.

Sai dai rahotanni sun ce ana kyautata zaton feshin wani maganin da aka yi ne a sabon gidan ya yi sanadiyyar mutuwarsu.

Wani na kusa da iyalan ya shaida wa kamfanin dillanci labarai na Najeriya (NAN) cewa sun rika jin wari sosai bayan kwana daya da iyalan suka shiga sabon gidan

Don samun labaranmu ta Whatsapp ka rubuto YES a SMS zuwa 08087645001. Shiga cikakken shafinmu. www.isyaku.com 

BBC

Post a Comment

RUBUTA SHARHI KO RA'AYINKA KAN WANNAN LABARI

Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN