Buhari ba Allah ba ne, tsige shi za mu yi - Jagaba

Wani dan majalisar wakilan Najeriya ya bayyana cewa babu abun da ake fama da shi a mulkin Shugaba Muhammadu Buhari da ya wuce yunwa da bakar wahala.
Kalaman Jagaba Adams Jagaba, wanda ke wakilatar Kachia da Kagarko daga jihar Kaduna, na zuwa ne bayan da majalisun kasa suka ka yi barazanar daukar mataki kan shugaban idan bai aiwatar da kudurorin da suka zartar ba.

A ranar Talata ne majalisun dokokin kasar suka amince da wasu kudurori 12 da suka ce wajibi ne gwamnatin Muhamadu Buhari ta aiwatar da su ko kuma su dauki mataki.

Sai dai har yanzu babu wani martani da fadar shugaban kasar ta mayar.

Amma rahotanni sun ambato wani dan majalisa mai goyon bayan shugaban, Muhammed Gudaji Kazaure, na cewa an dora wa wasu takwarorinsa alhakin fara yunkurin tsige shugaban, amma ba za su "bari ya yi tasiri ba".

Mista Jagaba ya ce idan har Shugaba Buhari bai aiwatar da kudurorin da suka bukata ba to za su tsige shi a bisa tsarin kundin mulkin kasa.

Ya kara da cewa ba sa shakkar yiwuwar hakan don "Buharin ba Allah ba ne kuma bai yi kama da Annabi ba, duk inda ya yi kuskure za mu take shi" in ji dan majalisar.

Zaman da majalisun dokokin suka yi dai na zuwa ne a lokacin da rashin jituwa ke kara fitowa fili tsakanin gwamnatin Muhammadu Buhari da kuma shugabannin majalisar.

Jerin kudurorin da suka cimma a zaman:



  • Kawo karshen kashe-kashe a Najeriya
  • A daina tsangwama da kuma muzguna wa wadansu 'yan majalisa
  • Gwamnati ta rika bin doka da oda
  • Shugaban kasa ya dauki mataki kan wadansu wadanda ya nada mukamai
  • Ya yi yaki da cin hanci da rashawa tsakaninsa da Allah
  • Ya daina sanya baki kan al'amurran da suka shafi majalisar
  • Majalisar dokokin kasar za ta fara tuntubar Majalisar Dinkin Duniya don ceto demokradiyyar Najeriya
  • Majalisar za ta tuntubi kungiyoyi masu rajin kare demokradiyya don ceto demokradiyyar kasar
  • Shugaban kasa ya magance matsalar rashin aikin yi da kuma talauci a kasar
  • Duka majalisoshin biyu sun nuna goyon baya ga shugabancin Bukola Saraki da kuma Yakubu Dogara
  • Kuma ba sa goyon shugabancin Sufeto Janar na 'yan sanda Najeriya Ibrahim Idris
  • Majalisa za ta dauki mataki kamar yadda tsarin mulki ya ba ta dama, idan aka ki yin wani abu.
Wadansu na ganin barazanar daukar matakin da tsarin mulki ya ba su kamar yadda suka yi ikirari zai iya hada wa da yunkurin tsige Shugaba Buhari

A ranar Litinin 'yan sandan kasar suka gayyaci Shugaban Majalisar Dattawa Sanata Bukola Saraki domin amsa tambayoyi kan zargin daukar nauyin 'yan fashi da makami a mahaifarsa ta jihar Kwara.
Sai dai daga bisani Sanata Saraki ya ce sun shaida masa cewa sun janye gayyatar, kawai suna bukatar "ya amsa ne a rubuce".

Rahotanni sun kuma ce an rage yawan jami'an tsaron farin kaya da ke bin tawagar Saraki da kuma Kakakin Majalisar Wakilai Yakubu Dogara, da kuma mataimakansu.

Wannan batu ne kuma ya sa kungiyar tsoffin 'yan sabuwar PDP, wacce Saraki da Kakakin Majalisar Wakilai Yakubu Dogara ke kan gaba a ciki, suka ce sun dakatar da tattaunawar da suke yi da gwamnatin kasar da kuma jam'iyyar APC.

Suna dai zargin cewa an mayar da su saniyar-ware ne tare da yi musu bi-ta-da-kulli, a gwamnatin da suka taimaka aka kafa.

A baya dai gwamnatin ta sha musanta wannan zargi.

Don samun labaranmu ta Whatsapp ka rubuto YES a SMS zuwa 08087645001. Shiga cikakken shafinmu. www.isyaku.com

#BBC

Post a Comment

RUBUTA SHARHI KO RA'AYINKA KAN WANNAN LABARI

Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN