Sojin Turkiyya sun halaka 'yan ta'addan PKK 4448 a Afrin

Akalla 'yan kungiyar ta'adda ta PKK 4448 ne sojojin Turkiyya suka aika barzahu a yankin Afrin kasar Sham,tun a lokacin da suka fara da kaddamar da farmakan tabbatar tsaro na "Reshen Zaitun" a yankin.

Ma'aikatar tsaron Turkiyya ce ta yi bayani game da hare-haren "Reshen Zaitun" da sojojin kasar Turkiyya suka kaddamar a yankin Afrin na Sham tun a ranar 20 ga watan Janairun bana, da zummar ganin 'yan ta'addar PKK/KCK/PYD-YPG da na DEAÅž da kubuto yankunan 'yan uwa Musulmai daga zalunci da cuzgunawar haramtattun kungiyoyin.

A cewar bayanin,tun farkon Hare-haren na "Reshen Zatun" ya zuwa yau,sojojin Turkiyya 54 suun yi shahada inda wasu 223 kuma suka jikkata.

Ana ci gaba da lalata bama-baman da aka binne a yankin Afrin,wanda sojojin Turkiyya da dakarun Free Syrian Army suka kubutar a ranar 18 ga watan Maris na bana.

A jimillance a lalata bama-bamai 373,wadanda 159 an kera su da hannu.

Sojojin Turkiyya tare da tallafin Hukumar ba da tallafi da agajin gaggawa ta dake karkashi ofishin Firaministan Turkiyya (AFAD),Hukumar Red Crescent ta Turkiyya da kuma wasu kungiyoyin agaji na Majalisar Dinkin, na ci gaba safa da marwa don ganin rayuwa ta sake dawowa daidai a yankin na Afrin.

An sanar da cewa za a ci gaba da kara kaimi wajen kaddamar da hare-haren na "Reshen Zaitun" har sai an ga bayan illahirin 'yan ta'adda,samar kwanciyar hankali da zaman lafiya mai dorewa a karkashin inuwar karamci da kuma dokokin kasa da kasa.

Don samun labaranmu ta Whatsapp ka rubuto YES a SMS zuwa 08087645001. Shiga cikakken shafinmu. www.isyaku.com

#TRT
Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN