Type Here to Get Search Results !

Aikata ba daidai ba da karamar yarinya a Badariya, Kotu ta dage zamanta

An ci gaba da sauraron shari'ar wani dan kabilar Igbo da ake zargi da aikata ba daidai ba da wata karamar yarinya a unguwar Badariya makonnin baya a babban Kotum Majistare ta 1 da kegarin Birnin kebbi.

'Yan makonnin baya ne wasu mutane suka tayar ta 'yar hayaniya bayan sun yi zargin cewa wanda ake zargin yana aikata ba daidai ba a unguwar.

Amma wata majiya ta shaida mana cewa tuhumar da mahukunta ke yi masa ba na aikata fyade bane, tuhumaa ce da ke da alaka da zargin yaudarar karamar yarinya da aikata ba daidai ba.

Lauyan wanda ake zargi ya gabatar da hujjoji daga littafan shari'a na dalilai da zai sa Kotu ta yi watsi da karar.

Amma Alkalin Kotun ya dage sauraron shari'ar har zuwa ranar 15 ga watan Mayu 2018 yayin da aka sake tasa keyar wanda ake zargin zuwa Kurkuku

Don samun labaranmu ta Whatsapp ka rubuto YES a SMS zuwa 08087645001. Shiga cikakken shafinmu. www.isyaku.com

Top Post Ad

Below Post Ad

Shiga group dinmu na WhatsApp domin samun labaran mu kai tsaye LATSA NAN
Domin zama Wakilin mu a garin ku LATSA NAN
Domin aiko Sako/Labari/Korafi LATSA NAN
Domin samun labaran mu a Facebook LATSA NAN
Domin samun labaranmu a Twitter LATSA NAN