Kasashen duniya sun fara kaurace wa kayan da Isra'ila ke samarwa bayan kiran da Erdogan ya yi

Sakamakon kiran da Shugaban Kasar Turkiyya Recep Tayyip ErdoÄŸan ya yi, Kasashen Musulmi na duniya sun fara kauracewa kayayyakin da Isra'ila ke samarwa.

A ranar 20 ga watan Mayu ne Shugaba Erdogan ya ziyarci kasar Bosniya inda ya gana da Turkawa da ke kasashen waje kuma a lkacin da ya ke kan hanyar dawo wa ya yi bayani ga 'yan jaridu.

A jawabin na sa Shugaba ErdoÄŸan ya tabo batun Zalunci da rashin adalcin da Amurka ta yi na mayar da ofishin jakadancinta da ke Tel Aviv zuwa Kudus. 

Da aka tambayi ErdoÄŸan ko za a yi aiki da kiran da suka yi na a kaurace wa Isra'ila da kayayyakinta kamar yadda Kungiyar Hadin Kan Kasashen Musulmi OIC suka bukata sai ya bayar da amsa da cewa, a matsayinsu na shugabannin kungiyar OIC sun yi kira ga Kasashensu da su kauracewa kayayyakin da Isra'ila ke samarwa. 

Shugaba ErdoÄŸan ya ci gaba da cewa, yana fata dukkan kasashe mambobinn OIC za su yi aiki da wannan kira tare da daina sayen duk wani daga hannun Isra'ila.

ErdoÄŸan ya kuma ce, Turkiyya ma za ta dauki mataki hakan inda za su duba duk wata alaka da suka kulla da Isra'ila a fannon kasuwanci da tattalin arziki. 

Shugaban na Turkiyya ya ce da zarar an kammala zabukan 24 ga watan Yuni za su fara aiki a kan haka.

Don samun labaranmu ta Whatsapp ka rubuto YES a SMS zuwa 08087645001. Shiga cikakken shafinmu. www.isyaku.com

#TRT 
Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN