An
bayyana karuwar mutuwar wasu mutane biyu bayan kamuwa da cutar Ebola a
Jamhuriyar Demokradiyar Kongo bayan sake buluwar cutar da ta yi
sanadiyar rayuka 28 kawu yanzu.
Hakika,
al’umar kasar sunki bin shawarwarin da aka basu domin kare kamuwa daga
cutar inda suke ci gaba da samar da naman biri a babban kasuwar
Mbandaka.
A
hirar da manema labarai suka yi da wata mata mai suna Carine, ta
bayyana musu cewar “Mun ki daina cin naman biri duk da an ta’alaka shi
da cutar Ebola, mun kasance masu cin naman biri shekara da shekaru, ba
zamu daina ba a yanzu”
Masana
wadanda suka yi bincike a lokaci da cutar ta fara bulla a shekarar 1976
sun bayyan cewar, an kamu da cutar ne daga jemagu da namun daji da
mutanen yankin ke ci kamar su birai da makamantarsu.
Don samun labaranmu ta Whatsapp ka rubuto YES a SMS zuwa 08087645001. Shiga cikakken shafinmu. www.isyaku.com
#TRT
Tags:
DUNIYA